MARGAYE! Gyara kimtsi da kyau! Takawarka lafiya dan toron giwa!
Wannan shi ne kirarin da maroka suka yi ta antayowa a fadar mai girma Sarkin Nasarawar Kaduna yayin da ake nada shugaban Kungiyar Furodusoshi ta Jihar Kaduna, Alh. Ashiru Sani Bazanga, a matsayin Danmasanin Nasarawa. An fara gudanar da bikin nadin sarautar da misalin karfe 10 na safiyar Asabar, 19 ga Yuli, 2003.
Alh. Ashiru yana daya daga cikin mutane 16 da Sarkin na Nasarawa ya yi wa nadin sarautu daban-daban a karkashin masarautarsa.
Da yake zantawa da wakilinmu jim kadan bayan nadin nasa, sabon Danmasanin godiya ya fara yi wa Allah Madaukakin Sarki da ya zabe shi daya daga cikin mutanen da ake hangen suna da mutunci da har za a dora masu irin wannan babban nauyi na mulkin jama'a. Ya kara da jawo hankalin jama'a da su ba masarautun gargaji hadin kai, tare da ba su shawarwari na kwarai don su samu sukunin sauke nauyin da aka dora masu tare da kare hakkokin talakawansu ba tare da nuna kabilancin yare ko bambancin addini ba.
Daga karshe ya yi godiya ta musamman ga shugaban Karamar Hukumar Danja ta Jihar Katsina, Alhaji Bishir Lawal Danja, wanda ya samu halartar bikin tare da tawagarsa. Ya kuma yi godiya da ban-gajiya ga 'yan'uwa da abokan arziki da suka goya masa baya suka halarci bikin.
Wadanda suka samu halartar bikin daga cikin 'yan fim sun hada da shugaban Kungiyar Furodusoshi ta Jihar Kano, Alh. Ibrahim Mandawari, Shehu Hassan Kano, Dan'azimi Usman (Dafe-Dafe), Saminu M. Mahmud, Yahuza A. Ilu, Rabi'u Rikadawa, A.S. Mohammed, Abdullahi Tasiri, Aliyu Abdullahi Kabala, Nuhu Garba Isah, Awwalu Marshal, da kuma Nasiru Dan Maliki. An dai tashi taron lafiya da misalin karfe 1:15 na rana.
Shi kuwa Danmasani, sai mu ce Allah ya taya shi riko.
Ban saki Rabi Mustapha ba, cewar mijinta
Daga ALIYU A. GORA II,
a Kaduna
ALHAJI Yahaya Abubakar ya karyata ji-ta-ji-tar da ake ta yadawa cewa wai aurensa da zabiyar zabiyoyin finafinan Hausa Rabi Mustapha ya mutu.
Ita dai Rabi, wadda ta yi aure da Alh. Yahaya har ta haihu a Abuja, ta janyo surutai a industiri din Kano yayin da 'yan fim suka dade suna ganinta a cikinsu cikin 'yan kwanakin nan. Wasu sun ce sun gan ta a situdiyo tana waka kamar da, wasu kuma suka ce sun gan ta a wuraren bikin auren 'yan fim. Wannan ya sa wasu suka rika baza ji-ta-ji-tar cewa an sako ta ne, shi ya sa ta dawo fagen shirin fim.
Da yake yi wa wakilinmu bayani kan al'amarin ta wayar tarho, Alhaji Yahaya, wanda ma'aikacin gwamnati ne, ya bayyana cewa mutane daga wurare daban-daban sun sha bugo masa waya suna neman karin bayani daga gare shi game da zargi da suka ji ana yadawa a gari cewa wai ya saki Rabi. Ya ce kuma mata da dama daga garuruwa kamar Gusau, Kebbi, Filato, Kaduna da dai sauransu sun je har gidansa a babban birnin tarayyar don su gane wa idonsu idan ta fita din.
A cikin bayanin nasa, ya ce ya san duk irin bayanin da ya sha yi wa masu zuwa da kansu, da yawa daga cikinsu ba za su gamsu ba, ba don komai ba kuma sai don a lokacin ita Rabi ba ta gidan, tana Kano wajen iyayenta. Haka kuma ya kara da cewa abin da ya fi tayar masa da hankali shi ne irin yadda da yawa daga cikin 'yan fim suke bugo masa waya cewa wai sun samu labarin cewa ya saki amaryar tasa, har ma wasu daga cikin 'yan fim din sun yi tattaki har zuwa inda yake don su tabbatar da gaskiyar lamarin. Alhaji Yahya ya ce gaskiya abin da ke faruwa shi ne, tun da ya auri Rabi ba ta taba zuwa ganin gida ba har ta haihu. Bayan ta haihu ne kuma sai ga sako an aiko cewa mahaifiyarta ta haihu. Saboda haka, a cewarsa, ya tura Rabi zuwa Kano don ta halarci bikin sunan, sa'annan kuma ya ba ta damar ta hada da hutun ganin gida, wanda ya ce ta kwashe fiye da wata daya a Kano tana hutawa tare da iyayenta.
A cewarsa, babu mamaki, wannan zaman ne wasu suka yi amfani da shi suke yada irin wannan mummunan zargi. A karshe ya jawo hankalin masu yada irin wannan ji-ta-ji-tar da su ji tsoron Allah su daina yada maganar da ba su da masaniya a kanta. Ya kara nanata cewa, "Aurena da Rabi Mustapha yana nan daram."
Komawa babban shafinmu  Komawa saman wannan shafin