ALLAHU Akbar! Da misalin karfe 5:30 na yammacin ranar Lahadi, 1 da Satumba 2002 ne Allah cikin ikonsa ya yi wa shahararren daraktan nan Alhaji Adamu Halilin rasuwa. Ya rasu a gidansa da ke lamba 19, Kagoro Close, Sabon Garin Tudun Wada, Kaduna, bayan wata jinya mai tsawo da ya yi fama da ita. Marigayin, wanda muka taba yi wa lakabi da "baban daraktocin finafinai" a fitowarmu ta watan Agusta, 2000, ba bako ba ne ga makarantanmu, musamman 'yan fim na da da na yanzun.
Mai shekaru 66 kafin rasuwarsa, Alhaji Adamu Halilu ne dan Arewa na farko da ya fara zuwa Turai ya karanto aikin fim cikin shekarun 1950. Ya kuma rike manyan mukamai a karkashin wannan aikin, wadanda suka hada da Babban Darakta na Sashen Majigi na Gwamnatin Tarayya (Federal Film Unit) da kuma Manajan Darakta na farko a Hukumar Shirya Finafinai ta Nijeriya (Nigerian Film Corporation).
Marigayin ya ba da gudunmuwa ga harkar fim da za a iya cewa babu kamarsa a kasa baki daya wajen shiryawa, ba da umarni da kuma jagorantar manyan hukumomin gwamnati kan wannan aiki. Shi ne kadai talikin da ko dai ya shirya ko ya ba da umarni ko ya yi duka biyun wajen aiwatar da finafinai akalla 80 na Turanci da Hausa a karkashin gwamnatocin da suka gabata. Sun hada da Shaihu Umar, Black Heritage, Kanta of Kebbi, Baban Larai, Moment of Truth, da sauransu. Shirin Baban Larai shi ne fim na farko da aka shirya da Hausa.
Haifaffen garin Garkida da ke cikin Jihar Borno, Alhaji Adamu Halihu ya karbi lambobin yabo masu yawan gaske daga hukumomin gwamnati na kasar nan sakamakon irin gagarumin gudunmuwar da ya bada a harkar fim na tsawon shekaru akalla 40. Lambar yabo ta baya-bayan nan da ya karba ta hannun tsohon shugaba kasa Janar Buhari ita ce wadda Cibiyar Adana Kayan Tarihi ta Arewa (Arewa House) ta Jami'ar Ahmadu Bello, Zariya, ta ba shi a lokacin rufe bikin baje kolin finafinai da littattafai da kayayyakin al'adun gargajiya da fasaha da ya gudana cikin watan Maris, 2001 a Kaduna.
Daraktan ya mutu da burin shirya ingantattun finafinan tarihi da suka shafi rayuwar Sarauniya Amina ta Zazzau, Sarki Bagauda na Kano, Mai Idris Alooma na Borno, da Jihadin Shaihu Usman Danfodiyo.
Ya rasu ya bar mace daya, 'ya'ya 11 da jikoki shida. Dimbin jama'a da wakilan hukumomin gwamnati da masu zaman kansu sun je gaisuwar ta'aziyya ga iyalan mamacin. A cikinsu akwai Nigerian Film Corporation (NFC), National Council for Women Societies (NCWS), wasu membobin MOPPAN, Sadiq A. T/Balewa, matar gwamnan Jihar Kaduna, Hajiya Asma'u Makarfi, tsohon shugaban Hukumar Shirya Finafinai ta Nijeriya Mista Brendam Shehu, da tsohon Minista Maccido Dalhatu.
Har ila yau akwai irin su Ambasada Mahmud Yahaya, Alhaji Musa Bello, Alhaji Yusuf Hamisu Abubakar, Hajiya Laila Dogonyaro, Hajiya Maisarari Chanchangi, wasu matan tsofaffin gwamnoni da suka hada da matar Dabo Lere, matar Buba Marwa, matar tsohon gwamnan Bauchi Mshelia, da matar Hamza Zayyad wadanda suka tafi tun da farko-farko. Akwai manyan mutane da kungiyoyi da dama wadanda ba mu ambato ba saboda yawansu kuma har ya zuwa lokacin rubuta wannnan rahoton kungiyoyi da al'ummar kasa ba su daina kai gaisuwar ta'aziyyar ba ga iyalan shi marigayi Alhaji Adamu Halilu. Allah ya jikansa, amin.
Komawa babban shafinmu  Komawa saman wannan shafin