Daga WAKILINMU
WASU 'yan shekarau kadan da suka wuce, fitaccen daraktan nan da ke Jos, Magaji Mijinyawa, yana zaune a wani falo na furodusa Sani Muhammad Sani, shi kuma furodusan yana cikin uwardaki sa'annan uwargidansa Usaina tana safa da marwa tsakanin kicin da sauran bangaren gidan domin ta ga mijinta da amininsa sun samu maganin yunwa. Tana yi tana rera wakoki daban-daban. Magaji ya kame a kan kujera kamar gunki yana sauraren wakokin. Ya kasa motsawa. Can sai ya yi wuf! ya tashi tsaye ya kwala wa mai gidan kira. Ita kanta Usaina sai da ta tsaya cak! a cikin tafiyarta. Sani ya fito da sauri, ya dauka wani abu ne ya faru.
Daga nan tunanin barin matarsa ta yi wakokin finafinansa ya shiga zuciyar Sani. Amma abin mamaki duk da cewa Magaji ne ya kawo tunanin, shi Magaji bai bai wa Usaina waka ta yi masa a cikin fim ba ko da guda daya ce, sai dai kullum ya samo karin waka sai su ukun su zauna su yi ta yi a gidan.
To, kowane fasihi yana da mai neman tauye shi. Usaina ta sha gamuwa da kulle-kullen mahassada wadanda suka dinga kushe muryarta saboda manakisa. Duk da haka, da yake Hausawa sun ce idan rana ta fito tafin hannu ba ya kare ta, Usaina ta samu daukaka, domin fa ta rera dimbin wakokin fim. Har ga shi a yau an wayi gari Farida Adams, 'yar wasa a Jos, tana cewa, "Da zan samu yadda nake so a harkar fim da sai na ce babu muryar mawakiyar da zan hau a cikin fim sai ta Usaina."
A lokacin da za a yi wani fim mai suna "Dan Jos," furodusan ya ce shi muryar Usaina yake so a fim din. Sai kuwa mahassada suka shiga aikinsu, suka matsa masa a kan cewa kada ta yi wakar, wanda hakan bai rasa nasaba da artabun da mijinta Sani Muhammad Sani yake yi da wasu daga cikinsu. A karshe dai cewa furodusan ya yi idan dai ba ita za ta yi wakokin ba sai dai ya yi fim din babu waka. Ya hakikice musu. Amma duk da haka sai da wasu mazugan suka yi munafinci a lokacin da Sadi Sidi Sharifai ya iso Jos domin yin wakokin, kulle-kullensu suka yi nasara, a karshe dai ba da ita aka yi wakokin ba.
Usaina Muhammad Sani 'yar shekaru 26 ce. Ita ce uwargidan furodusa, darakta, kuma marubuci Sani Muhammad Sani. 'Ya'yansu hudu cikin makarantar 'Jos Markazul Tarbiyyatul Islam,' Jos. Usaina, wadda ta yi aji uku a GSS Jos ta bari, ba ta yi kama da shekarunta ba; idan ka gan ta sai ka dauka 'yar shekaru goma sha ce!
To amma menene asalin abin da ya jawo hankalinta a kan yin wakokin? "Yawancin wakokin da na rubuta aka yi su a cikin finafinai asalinsu na yi su ne domin mijina saboda sonsa da nake yi ya sa nakan zauna in rubuta wakoki da sunansa in fitar masu da kari in rera masa yana jin dadi. Wani lokaci ma idan da kananan kuraje a fuskarsa ina fasa su ina yi masa".
Misali da ta bayar daga cikin irin wadannan wakokin shi ne na fim din Hamza-Habib wanda ta yi kamar haka: "Sani, Sani, Sani kaunarka nake, wanda in kalle ka sai in ji wani dadi, idan na dube ka sai in ji wani haske.." Sai ta juya a fim ya zama "Darling, Darling…"
Usaina ba ta fara yin wakokin finafinai ba har sai da ta yi aure. Amma a lokacin da tana budurwa takan rubuta wakokin Mauludi, wakokin yabon Annabi, ba ma na makarantarsu kawai ba har na wasu makarantun. Akan zo a neme ta ta rubuta ta fidda kari ko ta rubuta.
"Amma kuma nakan yi idan a gidan biki ne a wannan lokacin, ko a cikin kawayena nakan rera wakoki ne a kan Sani Muhammad Sani," inji ta. "Ko da ni da kawayena muna rera wakoki, tawa kam a kan Sani nake yi."
Ta yi dariya ta ce, "Zan gaya maku dalilin wannan. Kamar, ni a mafarki na ga Sani, a nan muka hadu, da na gan shi a zahiri sai da na cika da mamaki, na kasa komai a ranar, ga shi kuma a unguwarmu yake. Ashe Allah zai sa shi ne mijina!"
A dalilin wakoki a gidan biki na 'yan'uwanta da take yi ya sa iyayenta suka hana ta yin waka, suna tsoron kada ta zama marokiya. "Kuma ba ba ni kudi ake yi ba fa. Ina yin su domin raha ne, domin 'yan'uwana na son in yi masu su ji dadi."
Wacce irin hanya Usaina take ganin za a iya bi domin samun wakoki ingantattu?
"Hanya ta farko ita ce mu daina gaggawar yin su domin mu gama mu shiga kasuwa," inji ta. Ta kara da cewa, "Shi fa mutumin da yake wannan harkar kamata ya yi ya natsu, ya fitar da kansa daga cikin wadanda za mu iya kira 'yan kasuwa, ya zama mai kishin fim. Domin shi dan kasuwa damuwarsa a yi a gama kudi ya shigo hannu, ba wai inganta abin ba. Indiyan nan fa da muke ta yabonsu bayan tsabagen kudin da suke kashewa, suna bai wa komai hakkinsa: darektan kida daban, mai rubutawa waka daban, wani lokaci ma mai fitar da kari daban, masu kida kuwa sun wuce a yi maganar mutum daya a kan keyboard, masu bushe-bushe daban, masu ganga daban masu rerawa daban; komai ma'aikacinsa ne zai yi. Sannan a dawo comfuta a yi ta faman harhada kidan da tace shi. Don me ba za su yi wa mutane fintikau ba?"
Usaina ta ce sai mun kasance masu juriya, dauriya da hakuri kafin mu fara hango kafarsu ma balle mu kamo su. Sannan mun tambaye ta ko me za ta iya ce wa mafiyoyin da suka yi mata bukulu a lokacin daukar wakokin "Dan Jos"? Sai ta ce, "Fada da abin da Allah ya ba wani, fada da kaddarar Ubangiji ne, fada kuma da kaddara ta Ubangiji fada ne da Allah. Su ci gaba da yi domin ba da ni suke yi ba da Wanda ya ba ni muryar ne, Wanda kuma ya ba ni basirar. Sannan kuma idan kana son ci-gaba ka nemi mahassada amma fa ba ka nema da bakin hali ba, ka neme su da kyawawan halaye to za ka ci gaba."
Zabiyar ta ce ita ba ta taba sanin cewa ta isa ba a cikin mawaka, sai da ta samu mahasaada. Sau da yawa 'yanmata sukan bi ta situdiyo ko gida domin kawantaka saboda jin dadin muryarta da suke yi. Shi kuma mijinta ya ce idan yana sauraron muryarta a kaset, musamman ma dai idan ya yi tafiya takan ba shi tausayi ne har ma ya ji yana son komawa gida.
Da kuma muka tambaye ta menene take yawan tunawa a cikin rayuwarta wanda ba za ta taba mantawa da shi ba, sai ta amsa, "Mijina. Domin akwai wata irin rayuwa da yake yi wadda ba kowa ne ke yin ta ba. Na san yana da zafin rai idan an taba shi amma kuma shi ba zai taba wani ba. Duk da muna rawa ni da yarana - rawa ta barkwanci fa - yana shigowa idan yara ne suke waka sai ya kama yin rawar. To wannan abu ne da ya sa muke son shi har ba ma so ya fita a gidan. Da ya dawo kuma sai ka ga mun ruga da gudu mun rungume shi. To irin wadannan abubuwan ne suka sa ba zan taba mantawa da shi ba har abada. Amma kuma fa idan ka gan shi sai ka dauka ba zai iya yin hakan ba." Ga masu son ci gabanta kuma ta ce, "Alhamdu lillahi na gode masu su ma. Allah kuma ya ba su daukakar da ba su taba tunanin za su samu ba. Allah kuma ya ba su zaman lafiya da iyalansu, idan kuma ba su da iyalan Allah ya ba su ko mace ko namiji. Haka ma wadanda suke tsoron in samu dama zan fi wadanda suke kuma Allah ya bar mu tare."