A yau fim ya fi wa'azi shiga zukata
In ji Malam Zakzaky a wurin kaddamar da KARBALA
Daga SANI MOH'D MAIKATANGA a Kano
AN bayyana cewa wasan kwaikwayo babbar harya ce ta shigar da sakonni a zukatan mutane, musamman ganin cewa ba sosai jama'a kan dauki wa'azi a halin yanzu ba.
Shugaban Rundunar 'Yan'uwa Musulmi a Nijeriya, Malam Ibrahim Yakub Al- Zakzaky ne ya yi wannan furucin a babban dakin taro na otal din 'Royal Tropicana', Kano, lokacin da ake kaddamar da wani fim da 'Yan'uwa Musulmi Mata (Muslim Sisters) suka shirya mai suna Karbala.
Taron kaddamawar da aka yi a ranar 13 ga Afrilu, 2002, an shirya yinsa ne a rufaffen dakin motsa jiki na 'Sani Abacha Sports Complex'' amma aka sami sabani lokacin da masu shirya taron suka sami labarin gwamnatin Jihar Kano ta shirya wani taro a wurin. "Gwamnatin dagutai ta nuna cewa za ta gabatar da wani taronta sai dai mu bari sai da yamma," inji Malam Zakzaky. Ya kara da cewa bayan an sanar da shi ne ya ce a je a kama wani wuri daban.
Cikin jawabin da ya gabatar, shahararren malamin ya ce tun farko ba fim aka yi niyyar yi ba, an nemi shawararsa ne kan abin da ya dace a yi don a samu kudin shiga maimakon a rika neman taimako daga 'Yan'uwa don gudanar da wani abu. Malam ya ce ya ba da shawarar a yi wasan kwaikwayo maimakon yawon zuwa wa'azin da ake yi; ta haka za a tunatar da 'Yan'uwa "tunda yawanci ba daukar wa'azi ake yi ba."
Dimbin jama'a, musamman 'Yan'uwa Musulmi (Muslim Brothers) magoya bayan Malam Zakzaky sun cika dakin taron da kuma harabar otal din. Duk da cewa an biya kudin shiga N100, wannan bai hana samun cinkoso ba a bangaren mata da kuma su kansu maza. Yayin kaddamar da fim din na Karbala an tara kudi a take sama da N600,000.
Daraktan fim din, Malam Bala Makosa Zariya, wanda kuma shi ne editan mujallar Nishadi, ya yi nuni da cewa an shirya wannan fim ne domin fadakar da 'Yan'uwa Musulmi da su farka". Kuma ya ce, "Ba fim ba ne irin na jahiliyya da sauran ke yi. A'a, wannan fim duk wanda ya kalle shi zai san cewa an shirya shi ne domin ci gaban Musulunci da al'ummarsa".
Ita kuwa furodusar fim din, kuma matar Malam Zakzaky, Malama Zeenat Ibrahim, a cikin jawabin da ta yi a wurin ta yaba da irin goyon bayan da maigidanta da kuma darakta Bala Makosa suka bayar. Ta kuma gode wa Mai Martaba Sarkin Gumel, Alhaji Ahmed Mohammed Sani, wanda ta ce sun sami shawarwari da taimako daga gare shi. Ta gode wa wani sarki da ta ce ke cikin Jamhuriyar Nijar, da Yariman Zazzau Alh. Mannir Ja'afaru, wanda ya taimaka da dawakai, da kuma duk wani wanda ke da hannu a cikin shirya fim din.
Tun farko bayan bude taro da addu'a an gabatar da wadanda su ne suka dauki nauyin shirya fim din na Karbala, wato kungiyar mata Musulmi da ake kira da sunan Muslim Sisters Islamic Movement of Nigeria da ke garin Zariya.
Daga cikin 'yan fim da suka halarci wurin akwai shugaban Kungiyar Furodusoshi ta Jihar Kano, Alhaji Ibrahim Mandawari, wanda ya sayi kwafen kaset daya a kan N5,000 a madadin kungiyar da yake shugabanta, Yakubu Ibrahim da kuma Rukayya Umar Santa.
Ita ma jarumar fim din, Malama Jamila, ta yi bayani inda ta ce sun sha wahala sosai wurin shirya Karbala. Ta kuma gode wa Malam Zakzaky da Malam Bala Makosa.
An tashi taron lami lafiya.
Komawa babban shafinmu  Komawa saman wannan shafin