Free Web Hosting Provider - Web Hosting - E-commerce - High Speed Internet - Free Web Page
Search the Web

Jagorar mujallun Hausa
FITOWA TA 33   Satumba 2002
BABBAN LABARI


BABBAN SHAFI
MU LEKA MU GANI
HIRAR MUSAMMAN
Wasiku
KU TAMBAYE SU
Rahoton Musamman
Rahoto
Malam Zurke
RA'AYIN MUJALLAR FIM
Bukukuwa
Sauran Labarai
Fitattun Taurari
Dangane Da Mu
Muhawara a Zauren YAHOO!GROUPS

Wannan wani zaure ne da aka kirkira a dandalin sadarwa na zamani, wato intanet.
An gina zauren ne a kan tsarin 'Groups' na babbar masana'antar sadarwa ta intanet da ke Amerika din nan mai suna Yahoo!
A wannan zauren namu mutane suna tattaunawa ne musamman a kan finafinan bidiyo na Hausa wadanda ake yayin su yanzu.

JE KA TA NAN


Inda za ka samu tsaffin mujallun Fim
 
Je ka Bangon Fim ta 31
Bangon Fim ta 30
Bangon FIM ta 29
Bangon FIM ta 28
Bangon FIM ta 27
Tallar sabon fim din da ya fito!

NORTHERN STAR FILMS

KE GABATAR DA

GAGARABADAU Fostar fim din kenan

Shiryawa: MUJALLAR Fim

Darakta HAFIZU BELLO

Wasa: Sadiya Abdu Rano, Musbahu M. Ahmad, Sani Moda, Aliyu A. Gora, Hindatu Bashir, Isa Ja, A'isha Ibrahim, Mika'il Hassan 'Gidigo,' Baban Mulika, Shu'aibu 'Kumurci', Ashiru Bazanga, Saratu Gidado, Shehu Kano, Galin Money, d.s.

Labari/Tsarawa: Iro mamman;

Daukar Hoton Bidiyo: Yahaya Skito

BABU IRINSA!

Wasu matafiya ne Allah ya hada su tafiya a tsohuwar motar Direba Moda. Kowanensu yana da MU LEKA MU GANIn yadda ya kamata motar ta rika tafiya: wasu na kukan ana bata lokaci, wasu na cewa a rage gudu...

Can a kan hanya, yaran Gagarabadau (su Kumurci) sun tare hanya suna fashi...

Labari ne na soyayya, ban dariya, tada jijiyar wuya, da ban tsoro...

Idan har ka kalli fim din ba ka yi dariya ko ka ji taraddadin sharrin basawan Gagarabadau ba, to za mu biya ka kudinka! Ka tuntube mu ta e-mail dinmu don ka samu naka

 


In kana son mu aika maka duk lokacin da muka canza shafin nan
    
   Za mu rike sirri  

by ChangeDetection

'Yan fim za su shirya babban taron kara wa juna sani

Farfesa
Farfesa Abdallah Adamu
Daga IRO MAMMAN a Kano

BISA la'akari da yadda wasu jama'a suke yi wa harkar fim mugun kallo, 'yan fim na Kano suna nan sun fara share fage don gyara fuskarsu ta hanyar shirya wani gagarumin taron kara wa juna sani.

Wannan ya biyo bayan taron da Cibiyar Nazarin Hausa ta Jami'ar Usmanu Danfodiyo ta shirya a Sakkwato a watan Yuli na bana inda manazarta da jama'ar gari suka ragargaji harkar fim suna cewa tana bata tarbiyya.

Wata majiya ta ce taron da ake shirin yi a Kano zai tattaro masana daga jami'o'i da sauran manyan makarantu, da jama'ar gari, da kuma su kansu masu harkar fim din. "Muna ma da nufin gayyato masana daga kasar waje," inji majiyar.

Ya zuwa yanzu har an yi zama guda uku a ofishin 'Moving Image' da ke kan Titin Zoo a Kano, inda a taro na baya-bayan nan, wanda aka yi a ranar Lahadai, 25 ga Agusta, aka zabi masanin adabi din nan Furofesa Abdalla Uba Adamu a matsayin shugaban kwamitin tsare-tsare na taron.

A zaman da aka yi kwanan nan din, 'yan fim da dama (musamman furodusoshi da daraktoci) sun hallara, kuma sun tattauna matsalolin da ke addabar sana'arsu da kuma yadda suke jin taron kara wa juna sanin zai kasance. Mun sami labarin cewa a wurin, Furofesa Abdalla ya nuna bukatarsa ta maida taron ya zama dandalin ilimintar da juna ba na sukar juna ko fashe haushi ko taka rawar muguwar rarrabuwar da ta sha kan harkar fim a Kano ba.

Shi dai Furofesa Abdalla, an nada shi ciyaman ne saboda dacewarsa, sa'annan saboda shi ba memba ba ne na wani gungu a cikin sansanonin siyasar harkar fim. Haka kuma kasancewarsa malamin jami'a da ake girmamawa zai iya ba taron da za a yi karin daraja a gun masana.

Mun ji cewa za a kai cikin farkon badi kafin a yi taron, domin Abdalla da sauran shugabanni suna so a yi tsari mai kyau kafin lokacin. An tsayar da Asabar, 7 ga Satumba, 2002 a matsayin ranar da za a yi zama na gaba inda za a tattauna kan irin jawaban da ake son a yi a taron na kara wa juna sani. Dillalan kaset za su zabi shugabanni Daga ASHAFA MURNAI BARKIYA a Kano

'YA'YAN Kungiyar 'yan kasuwa masu sayar da kaset na bidiyo da rikoda na Jihar Kano za su zabi shugabanninsu a ranar Lahadi, 8 ga Satumba, 2002.

Wakilinmu ya gano cewa ko shaka babu za a kara sosai idan aka yi la'akari da jerin sunayen 'yan takarar mukamai, musamman mukamin shugaban kungiyar. Mutum uku ake jin za su kara wajen neman zama shugaba; su ne: Alhaji Idris Danzariya, mai kantin sayar da kaset da shirya fim na 'El-Duniya,' da Alhaji Sama'ila T.M. wanda ke sayar da kaset na rikoda a Kasuwar Kofar Wambai, da kuma Malam Tukur mai saida kaset na rikoda a Kasuwar Kofar Wambai.

Za a yi zaben ne a gidan sinima na Oriya da ke Kofar Wambai, Kano. Tuni dai 'yan takarar mukamai daban-daban suka dinga yin kamfen a wurin 'yan'yan kungiyar, kowane da alkawuran wasu abubuwa da yake ganin sai an yi su kafin kungiyar ta samu ci-gaba. Ita dai wannan kungiya, ta dade tana cikin rikici na shugabanci, ta yadda har ma ta kasu gida-gida, wasu 'ya'yanta na cewa ba su yarda da wasu ba. Kila in an yi wannan zabe a samu sa'ida. Furodusoshin Gombe sun dinke barakarsu
Daga SANI AHMED SASA a Gombe

BARAKAR nan da ta addabi Kungiyar Furodusoshi ta Jihar Gombe, wadda muka ba ku labarinta a watan jiya, ga alama yanzu ta kau, sakamakon zaben sababbin shugabannin wucin-gadi na kungiyar da aka yi kwanan nan.

Furodusoshi 20 ne suka yi zaben yayin da hudu suka ki jefa kuri'arsu, wato suka yi jemage kenan.

Shugabannin su ne: Kasimu A.Y. Musa a matsayin ciyaman; mataimakin shugaba - Umar Dan Sadiq; ma'aji - Umar Ardo, sai jami'in hulda da jama'a - Sa'adu Lawan.

Shugaban, wato Kasimu, haifaffen Gombe ne wanda ya yi makarantun 'Central Primary' da 'Comprehensive Day Secondary' a Gombe. Bayan kammala karatunsa na sakandare sai ya fada harkar kasuwanci yana saida magani, daga baya kuma ya bude kamfanin shirya fim mai suna 'M.D.V. Videos'. Ya fara fitowa a fim a farkon shekarun 1990 da fim mai suna Maci Amana.

Da mujallar Fim ta tambaye shi batun alakarsa da sauran furodusoshin jihar yanzu da yake ya zama shugabansu, sai ya ce, "Tun tuni ina da kyakkayawar alaka da dukkan furodusoshi har ma da shi Sadiq Dan Nana" - wanda suka yi rikici da shi kwanan baya.

Ya dora laifin rikicinsa da Sadiq a kan Sadiq din, har ya ce Sadiq "bai dace ya yi shugabanci ba."

Kasimu ya yi kira ga dukkan 'yan fim na Jihar Gombe da su ba shi hadin kai don ya cimma kudirorinsa.

Da yake kwatanta ci-gaban shirin fim a Gombe da Kano kuwa, sai ya ce, "Muna da hazikan 'yan wasa da yawa. In da a ce muna da abu biyu, da yanzu mun yi nisa: na farko shi ne da masu kudinmu za su sa kudinsu, sannan kuma a ce gwamnati ita ma ta taimaka, da wallahi babu wani abu da 'yan fim na ko'ina za su nuna mana."

Kasimu ya bugi kirji a kan gasar finafinan Hausa ta kasa da ake shirin yi a Kano cikin Disamba, ya ce, "Tunda yanzu an rigaya an zabe ni a matsayin shugaba, to fa lalli ne duniya ta ji tsoron fim din da za mu fitar a wannan gasar. Kuma ina mai shaida ma cewa finafinan Gombe za su yi tasiri sosai, in har furodusoshinmu sun ba da hadin kai sosai."

A karshe ya yi kira ga abokan hamayyarsa kamar haka: "Kiran da zan yi a kan su wadannan 'yan tawayen shi ne su zo mu hada kai don ci-gaban harkar fim a Gombe. Kamar ita Hajiya Bebe Gafa, babu yadda ba mu yi da ita ba amma ta ki ba da hadin kai, ba mu dai san nan gaba ba."

Ita dai wannan kungiyar, an yi mata rijista ta jiha, amma dai satifiket din bai shigo hannu ba tukuna domin Kwamishinar Mata da Matasa ta jihar, wadda ya kamata ta sa hannu a kan satifiket din, ta tafi kasar waje. Duk da haka a ran 15 ga Yuli kungiyar ta samu takardar izini daga ofishin kwamishinar mai lamba MOWAYD/RCA/S/8/1, mai dauke da sa hannun Lawenji M. Laison, inda aka gaya wa kungiyar cewa ta ci gaba da aiwatar da harkokinta bisa doka da oda kafin a gama yin binciken tsaro a kanta.

Komawa babban shafinmu           Komawa saman wannan shafin