Bikin kanwar Sani Danja ya tara mutane
Daga SANI MOH'D MAIKATANGA
a Kano
DIMBIN ' yan fim ne suka yi wa fitaccen jarumi Sani Musa (Danja) kara suka halarci bikin auren kanwarsa Fatima (Ladidi) Musa wadda ta auri Abubakar Saminu Kura kwanan nan a Kano. Duk wanda ya halarci bikin ya san lallai Sani yana da masoya a cikin 'yan fim, domin kai ka ce bikin na aurensa ne.
An daura auren a a ranar Asabar, 6 ga Yuli, 2002 a unguwar su Sani, wato Tudun Murtala.
Mahalarta sun hada da Ali Nuhu, Ahmad S. Nuhu, Kabiru Maikaba, Tijjani Asase, Jazuli Kazaza, Rufa'i Kudi da Ali Gote. To amma kada mu yi tuya mu manta da albasa, babban abokin Sani, wato shahararren mawakin finafinai Yakubu Muhammad, yana wurin shi ma a matsayin kijin biki.
Jim kadan da daura auren, amarya ta bayyana mana farin cikinta kamar haka: "I am irin very happy in this day, kuma I am irin grateful to God Almighty Allah. Sannan ina godiya ga 'yan'uwana yadda suka tsaya wajen ganin komai ya tafi daidai. Allah ya saka masu da alkhairi, amin." Shi ma Sani ya yi godiya ga jama'ar da suka halarta, yana mai fatan Allah ya maida kowa gida lafiya. Ya bukaci kanwarsa ta bi mijinta sau da kafa kuma ta rike 'yan'uwansa tamkar nata.
Daga wurin daurin auren an dunguma zuwa 'Sani Abacha Youth Centre' inda aka shirya walima. 'Yan'uwa da abokan arziki sun halarci walimar. 'Yan fim a wurin sun hada da Hajara Usman, Kabiru Maikaba, Ummi Nuhu, Jamila Haruna, Rukayya Umar Santa, Maryam Umar Aliyu, Maryam Abubakar, Fati Bappa Fagge, Baba Sheriff, Ahmed M. Sasari, Rabi'u Ibrahim, Tijjani Paris, Suleiman Sa'eed, Sulaiman Gambo Awaisu, Yusuf Khalid, Musbahu M. Ahmad, Baballe Hayatu, da Ali Mai Dawayya.
Kabiru Maikaba ne ya bude taro da addu'a. Daga nan aka ci gaba da furta kalaman taya ango da amarya murna.
An kuma cashe da wakokin fim daban-daban a wurin. Maryam Abubakar (Jan Kunne) da Ale Mai Dawayya sun rera wakar cikin Darasi 2 mai taken "Duk Girmana Yau Sai Kin Sa Na Yi Kas"; Musbahu da Ummi Nuhu suka yi wakar Kansakali; Yakubu da Fati Bappa suka yi wakar "Mun Iya Renonmu Na Mata" ta cikin Rawani, kuma Sani Danja da Rukayya suka yi wakar cikin Jaheed. An yi tande-tande da lashe-lashe.
Wani abu mai jan hankali shi ne cashewar da amarya da ango suka yi lokacin da Yakubu yake wake su kuma jama'a suna ta yi masu liki. Sai wajen karfe 10 da wasu mintina na dare ne aka fara watsewa daga wurin.
Komawa babban shafinmu  Komawa saman wannan shafin