Ligidi na so a sake tsari don gyara lafawar kasuwa
Daga SANI MOH'D MAIKATANGA a Kano
A CI-GABA da 'yan fim suke yi na gano dalilan da suka jawo faduwar kasuwar finafinan Hausa da hanyar da za a bi a yi gyara, shahararren dan wasan nan Abdullahi Zakari (Ligidi), ya ce babu shakka harkar fim na Hausa za ta ci gaba, amma fa sai an yi gyaran da ya dace.
Lokacin da yake tattaunawa da Fim a Kano, Ligidi ya ce, "Akwai hangen ci-gaba amma kuma akwai bukatar gyara, saboda duk abin da kake yi da ma sai ka samu matsala. Daga baya kuma za ka ga alfanunsa in ka gano matsalar.
"Na tabbatar in har mun gyara kura-kuranmu samun ci-gaba ba sai an fada ba, domin da ma kasuwanci yana da wannan."
Malam Abdullahi ya lura da cewa a wannan harka akwai kurakuran da ake tafkawa, kuma ba za su kau ba har sai ana "samun hadin kai." Ya ce: "Ita wannan matsalar ba ta mutum daya ba ne - daga kan masu gabatar da finafinai, 'yan kasuwa, sai 'yan wasan da kuma su masu gabatar da wasannin wajen daukar wasan."
Ya yi nuni da yadda wasu mutanen ke ta antayowa cikin harkar fim barkatai babu tsari. "Ga shi muna samun wasu suna ta shigowa harkar, dole ne da ma duk abin da kake yi in dai har na jama'a ne, sai an samu wasu sun shigo, to amma shigowar tasu ba tsari, duk wanda zai shigo kamata ya yi ya biyo ta kafa mai kyau. Saboda da zarar wani abu na gyara ya taso sai a sanar da shi. Amma kawai kuma ga cunkushewar kasuwar finafinai a yanzu. Amma abin ba na mutum daya ba ne; kowa yana da laifi."
Ya kara da cewa in dai har ana so a ci gaba a harkar, "kamata ya yi mu san inda matsalar take, mu zauna kowa ya kaskantar da kanshi domin a yi wannan gyara. To amma ga shi an bar finafinai suna ta fitowa ba tsari barkatai, sannan da kuma ma rashin tsarin fim mai kyau.
"Kamata ya yi duk fim din da zaa yi a san yana da labari mai kyau, sannan kuma 'yan wasa sun san abin da suke yi. To in dai za mu yi haka to lallai insha Allahu kasuwa za ta gyaru."
Kuma a duk harkar da mutum ya sani, inji Ligidi, ana neman sani kuma ana neman hadin kai da tsari mai kyau. "Ya kamata duk wani mai wannan harkar ya zo domin a zauna a sami tsari mai kyau wanda duk wanda ya karya doka a hukunta shi. Kuma duk bin da mutane ba sa so mu guje shi ba mu yi ta yin abu daya ba - soyayya kawai. Dole mutane su ce ta gundire su.
"Tunda haka ne mu koma irin matsalolin da suke addabarmu mana, kamar makirce-makirce, cin amana da zamba. To ko soyayya ka sa kuma rawa da wakar ma a yi masu tsari da ma'ana."
Yakubu Lere ya yi amarya
Daga Wakilinmu a Zariya
Yakubu Lere
|
FITACCEN furodusan shirin Wasila, Yakubu Lere, ya kara mata, inda ya auri wata budurwa mai zama a Kaduna mai suna Habiba Mohammed Rilwanu. An daura aurensu a ran Asabar, 5 ga Oktoba, 2002, da misalin karfe 3:30 a gida mai lamba 58 da ke 'Aminu Road,' Tudun Wada, Zariya, a kan sadakin N10,000, kuma ango ya biya lakadan. 'Yan fim da dama sun halarci daurin auren, yawancinsu daga Kano, amma kuma angon ya ki gayyatar wasu manyan 'yan fim wai saboda bai shiri da su, ciki kuwa har da Sakatare-Janar na Kungiyar Furodusoshi ta Arewa, Malam Abdullahi Maikano Usman.
A ranar Lahadi ne kowa ya kama gabansa tare da yi wa ango da amarya fatan alheri da zaman lafiya. Muna taya su murna.
A gafarce mu
A Fim ta watan jiya, a filin "Mu Leka Mu Gani," Ibrahim Sheme ya ambaci cewa marigayi Alhaji Adamu Halilu dan Jihar Adamawa ne saboda dan asalin Garkida ne. To, an jawo hankalinmu ga cewa Garkida cikin Jihar Borno take kamar yadda muka rubuta a labaran da suka shafi marigayin a baya. Muna fatan za a gafarce mu kan wannan tuntuben alkalamin. Edita
Komawa babban shafinmu  Komawa saman wannan shafin