Free Web Hosting Provider - Web Hosting - E-commerce - High Speed Internet - Free Web Page
Search the Web

Jagorar mujallun Hausa
FITOWA TA 31   Yuli 2002
RAHOTO


BABBAN SHAFI
RA'AYI
Zuwa Ga Masu Karatu
Wasiku
Balaraba Muhammad (1983-2002) 
Rahoton Musamman
Rahoto
Malam Zurke
Ra'ayin Mujallar Fim
Bukukuwa
Sauran Labarai
Fitattun Taurari
Dangane Da Mu
Muhawara a Zauren YAHOO!GROUPS

Wannan wani zaure ne da aka kirkira a dandalin sadarwa na zamani, wato intanet.
An gina zauren ne a kan tsarin 'Groups' na babbar masana'antar sadarwa ta intanet da ke Amerika din nan mai suna Yahoo!
A wannan zauren namu mutane suna tattaunawa ne musamman a kan finafinan bidiyo na Hausa wadanda ake yayin su yanzu.

JE KA TA NAN


Inda za ka samu tsaffin mujallun Fim
 
Je ka Bangon Fim ta 30
Bangon FIM ta 29
Bangon FIM ta 28
Bangon FIM ta 27
Tallar sabon fim din da ya fito!

NORTHERN STAR FILMS

KE GABATAR DA

GAGARABADAU Fostar fim din kenan

Shiryawa: MUJALLAR Fim

Darakta HAFIZU BELLO

Wasa: Sadiya Abdu Rano, Musbahu M. Ahmad, Sani Moda, Aliyu A. Gora, Hindatu Bashir, Isa Ja, A'isha Ibrahim, Mika'il Hassan 'Gidigo,' Baban Mulika, Shu'aibu 'Kumurci', Ashiru Bazanga, Saratu Gidado, Shehu Kano, Galin Money, d.s.

Labari/Tsarawa: Iro mamman;

Daukar Hoton Bidiyo: Yahaya Skito

BABU IRINSA!

Wasu matafiya ne Allah ya hada su tafiya a tsohuwar motar Direba Moda. Kowanensu yana da ra'ayin yadda ya kamata motar ta rika tafiya: wasu na kukan ana bata lokaci, wasu na cewa a rage gudu...

Can a kan hanya, yaran Gagarabadau (su Kumurci) sun tare hanya suna fashi...

Labari ne na soyayya, ban dariya, tada jijiyar wuya, da ban tsoro...

Idan har ka kalli fim din ba ka yi dariya ko ka ji taraddadin sharrin basawan Gagarabadau ba, to za mu biya ka kudinka! Ka tuntube mu ta e-mail dinmu don ka samu naka

 


Mu mara wa mujallunmu baya

-Dr. Rasheed a bikin cikar Garkuwa shekara 2

Mujallar Garkuwa ta cika shekara biyu
Jagororin GARKUWA: Malam Kabir Assada da Dr. Malumfashi
Daga A ALIYU A. GORA II a Kaduna

AN yi kira ga daukacin al'ummar Arewa su ba da cikakken hadin kai da goyon baya ga ci-gaban kafafen yada labarai masu zaman kansu na yankin. Shugaban Tsangayar Fasaha da Addinin Musulunci ta Jami'ar Bayero, Kano, Dr. Abubakar A. Rasheed, shi ne ya yi wannan kiran a wurin taron bikin cika shekara biyu da kafuwar mujallar Garkuwa kwanan nan.

A bikin, wanda aka yi a dakin taro na Gidan Arewa da ke Kaduna a ranar Asabar, 8 ga Yuni, 2002, an kuma karrama wadansu muhimman mutane na arewacin kasar nan, ciki har da wasu fitattun 'yan wasan fim.

Dr. Rasheed, wanda ke magana a matsayinsa na babban bako mai jawabi a taron, ya ce, "Ya wajaba a gare mu mu sake tunani idan dai har muna so Arewa ta bunkasa ta kuma ci gaba. Jaridu da mujallu na daga cikin hanyoyin bunkasa al'umma, don haka ya zama wajibi ga 'yan bokon Arewa da masu kudin Arewa su agaza wa jaridun Arewa ta hanyar ba su tallace-tallace da kuma bude gidajen jaridu da mujallu da niyyar kare kai, ba da niyyar cin riba ta nan kurkusa ba."

Dr. Rasheed, wanda shi ne tsohon manajan-darakta na kamfanin buga jaridun New Nigerian da Gaskiya Ta Fi Kwabo, ya kuma yi kira ga marubuta da su dage wajen taimakon jaridu da mujallun Arewa da rubuce-rubuce masu ma'ana da wayar da kai. Ya ce su kuma masu karatu su jure wajen saye da karanta mujallu da jaridun da ake yi a Arewa a matsayin gudunmuwarsu don dorewar jaridu da mujallun.

Tun da farko sai da mawallafin Garkuwa, Dr. Ibrahim Malumfashi, ya karanto jawabin maraba inda ya yi amfani da wannan damar ya jawo hankalin 'yan Arewa a kan sanin muhimmancin karanta jaridu da mujallun Arewa. Ya ce ginshikin ginuwar kowace jarida ko mujalla yana samuwa ne kawai ta hanyar tallace-tallace. Ya kuma nuna takaici a kan yadda masu kudinmu suka fi son ba da talla ga jaridun Kudu, maimakon su ba na Arewa. Hakan, inji shi, yana ba da gagarumar gudunmuwa wajen rugujewar jaridu da mujallun Arewa.

A nasa jawabin, Alhaji Mustapha Idris, wanda ya wakilci shugaban taron, Manjo-Janar Muhammadu Buhari, ya amince da jawabin Dr. Malumfashi, inda ya yi kira ga 'yan jarida da cewa kamata ya yi su kira wani taro inda za a tattauna kan yadda za a shawo kan matsalolin da ke addabar jaridu da mujallun Arewa. A karshe kuma ya jawo hankalin 'yan Arewa a kan bai wa karanta mujallu da jaridun Arewa muhimmanci, ya ce kin yin hakan yana daya daga cikin abubuwan da suka sa 'yan Kudu suka tsere mana.

Da yake jawabi a taron, Shugaban Kungiyar Furodusoshi ta Jihar Kano, Alh. Ibrahim Mandawari, ya yi kira ga masu mujallun Hausa, musamman Ibrahim Malumfashi da Ibrahim Sheme, da su yi wa Allah su rika sa kishin addini a aikinsu na jarida. Ya ce sahabban Manzon Allah (s.a.w.) su ne farkon wadanda suka fara aikin jarida ta haryar ruwaito hadisai kuma ba su taba kauce wa gaskiyar abin da ya faru a zamanin Manzo ba. Mandawari ya yi roko ga hukumomin mujallun da su rika rubuta labaran ci-gaba a kan dan wasa maimakon buga mugun labari.

Taron ya samu halartar manyan baki daga sassa daban-daban na arewacin kasar nan, ciki har da Alhaji Abdullahi Gambo, wanda ya wakilci Gwamnan Jihar Kaduna. Daga cikin 'yan wasan da suka samu halarta akwai Ibrahim Mandawari, Aminu A. Shariff (Momo) da kuma wakilin Abida Mohammed, Adamu Sani. A karshen bikin an karrama wadansu mutane da suka hada da Shugaban Majalisar Dokoki ta Tarayya, Alhaji Gali Umar Na'abba, da gwamnonin jihohin Kaduna, Gombe, Neja, Zamfara, da Sokoto, sa'annan da 'yan wasa uku: Mandawari, Abida da kuma Momo. Haka kuma mujallar ta karrama wasu wakilanta: Zainab Muhammad Siddam, Kallamu Rugar Waje, da Umar Bandi Kofar Kware.

An tashi lafiya daga taron da misalin karfe 2:27 na rana.

Komawa babban shafinmu           Komawa saman wannan shafin