SHUGABAN Kungiyar Furodusoshi ta Arewa, Alhaji Hamisu Lamido Iyan-Tama tare sakataren kungiyar, Malam Abdullahi Maikano Usman, sun jagoranci wata tawaga ta 'ya'yan Kungiyar Furodusoshi ta Jihar Kaduna suka kai gaisuwar ta'aziyyar rasuwar shahararren darakta Alhaji Adamu Halilu, wanda ya rasu ran 1 ga Satumba 2002.
Tawagar, wadda ta kunshi sabon zababben shugaban Kungiyar Furodusoshi ta Jihar Kaduna, Malam Ashiru Sani Bazanga, ta isa gidan marigayin da ke layin 'Kagoro Close' a Tudun Wada, Kaduna, da misalin karfe biyar na ranar Asabar, 29 ga Satumba, 2002.
Bayan Maikano ya gabatar da furodusoshi ga iyalan mamacin, tare da jaddada juyayin rasuwarsa, sai furodusoshin suka yi wa mamacin addu'ar neman gafara da kuma rahamar Ubangiji.
Furodusoshin sun hada da Iyan-Tama, Maikano, Bazanga, Aliyu Abdullahi, Magaji Suleiman, Ahmed Alkanawy, Abubakar Ishaq, Nasiru Dan Bisallah, Murtala Aniya, Dr. Sani, da kuma wakilin mujallar Fim Aliyu Abdullahi Gora II.
A jawabinsa na karshe, Abdullahi Maikano Usman ya ce babu shakka rasuwar Alh. Adamu Halilu babbar asara ce ga dukkan masu shirin fim, musamman idan aka yi la'akari da gagarumar gudunmuwar da ya bayar wajen kyawawan shawarwari da ya bada wajen habaka darajar shirin fim. Maikano ya yi kira ga dukkan mai sana'ar shirin fim da ke arewacin kasar nan da ya ci gaba da yi wa marigayin addu'ar neman rahamar Allah.
Ta'aziyyar ta biyo bayan sanar da furodusoshin da wani furodusa ya yi cewa Allah ya yi wa Alhaji Adamu Halilu rasuwa. Da yawa sun bayyana mamaki, suka ce sam ba su san cewa ya rasu kusan wata daya da ya gabata ba.
Anya za a yi gasar finafinai ta Arewa a bana?
Daga WAKILINMU a Kano
A BISA dukkan alamu fitacciyar gasar finafinai din nan ta Hausa, wato 'Arewa Films Award' ta shekara ta 2002 za ta sami tangarda. Wannan kalami kuwa ya fito ne daga bakin babban jami'in masu shirya gasar, fitaccen daraktan nan Alhaji Abdulkareem Mohammed.
Da yake amsa tambayoyin mujallar Fim a a ofishinsa da ke kan titin 'Zoo' a Kano, shugaban na kamfanin editin na 'Moving Image' ya tabbatar da cewa a bana ba za a gudanar da gasar ba sai fa idan su masu shirya gasar sun sami wasu kamfanoni ko wani kamfani da zai iya daukar nauyin gudanar da bikin.
Ya yi nuni da irin kudin da kamfanin shirya gasar nasu mai suna 'Arewa Films Promotion' ya kashe a wajen shirya bikin na 2001, amma ya kasance abin bai yi wa aljihun kamfanin dadi ba.
An tambaye shi ko sun fara fafutikar neman mai daukar nauyin gasar, sai ya amsa: "Sosai kuwa. A yanzu din nan muna nan muna tattaunawa da kamfanin NASCO da kuma gwamnatin Jihar Bauchi". Ya kara cewa kuma muddin abin ya kankama daga daya daga cikin wadannan, to za a ji son buga tambarin shiri.
A karshe da aka tabo masa batun taron kara wa juna sani na kasa da kasa da za a yi kan finafinan Hausa, sai Alhaji Abdulkareem ya toge ya ki cewa komai bisa dalilin cewa shi dan kwamiti ne kawai. Duk da haka dai ya tabbatar da cewa a taron baya-bayan nan da aka gudanar, 'yan kwamitin taron sun cimma kudiri daya cewa za a rika yin taron a duk bayan shekara biyu.
Za a fara taron a cikin 2003, a tsakiyar shekarar ko kuma can wajen gabatowar karshenta, "ba don komai ba kuwa sai don mu yi wa taron kyakkyawan shiri," inji Malam Abdulkareem wanda har ila yau shi ne mawallafin mujallar Duniyar Fim.
Mahaifiyar Tsigai ta rasu
Daga SANI AHMED SASA, a Gombe
ALLAH ya yi wa mahaifiyar shaharriyar 'yar wasan nan Hajiya Hussaina Gombe (Tsigai) rasuwa. Mahaifiyar, mai suna Hadiza Wulaye, ta rasu a ranar Lahadi, 15 ga Satumba, 2002 bayan ta yi fama da rashin lafiya inda aka kwantar da ita a asibitin kwararru na Gombe.
Marigayiyar mai shekaru 65 a duniya ta bar 'ya'ya da dama, daga ciki har da ita Tsigai wacce ke yawan fitowa a fim tare da Rabilu Musa Danlasan (Ibro).
'Yan fim da dama sun halarci wurin karbar ta'aziyya. Daga cikinsu akwai Ibro da tawagarsa, sai Alhaji Damamusau da tasa tawagar, da furodusoshi da 'yan wasan fim na Gombe da dama.
Allah ya jikan marigayiyar, kuma ya ba magadanta jimirin jure wannan rashin, amin.
Komawa babban shafinmu  Komawa saman wannan shafin