WANI matashi mai ba da umurni a finafinai tare da wata shahararriyar 'yar wasan fim sun shiga tsomomuwa a kasar Iran a dalilin sumbatarsa da ta yi a bisa goshi, wanda hakan ya sa gwamnati ta maka su a kotun Musulunci a kan laifin sun yi laifin taba juna bayan ba muharramai ba ne.
A karkashin dokar shari'ar Islama wadda ake gudanarwa a Jamhuriyar Musulunci ta Iran din tun bayan da aka yi juyin-juya-halin da marigayi Ayatullahi Khomeini ya jagoranta a cikin 1979, an hana maza da mata su shafi jikin juna ko da ta hanyar gaisawa ce.
Sanin hakan ya sanya mahalarta wani babban bikin bada kyaututtukan gasar finafinai a birnin Yazad duk suka yi shiru kamar ruwa ya ci su da suka ga wata jaruma da ake girmamawa mai suna Gohar Kheirandish ta kai baki ta sumbaci goshin darakta Ali Zamani kuma ta kama hannunsa suka gaisa lokacin da ta mika masa kyautar da ya ci ta Gwarzon Darakta.
Abin ya faru ne a ranar Jumma'a, 27 ga Satumba, 2002.
Da yake kare kansa, an ruwaito Ali Zamani yana gaya wa wata jarida da ke fitowa kullum-kullum mai suna Efemad cewa, "Ni aka zaba a matsayin gwarzon mai shirya fim a bikin, kuma ni dalibi ne na marigayi mijin ita Kheirandish, to jin dadin nasarata ya sa har ta sumbace ni a goshi."
Shi da ita sun ba jama'a hakuri kan kuskuren da suka tafka, suka ce su kansu ba su san lokacin da kawai suka ji sun yi wannan abu ba har sai da suka yi din, kuma sam ba sun yi hakan ne domin su bakanta wa kowa rai ba.
"Sumbar da ta yi min kwatankwacin wadda uwa ke yi wa danta ne," inji Ali.
Sai dai kash! inda Gizo ke sakar shi ne su 'yan hisba (wato dogarawan tabbatar da bin dokar Islama) da suka halarci bikin ba haka suka kalli al'amarin ba. Shugaban 'yan hisba na birnin ya bada umurnin a cafke mutanen biyu a kan laifin sun aikata alfasha a gaban jama'a.
Tuni aka maka Ali Zamani a kotu, inda aka bada belinsa a kan kudi kamar dalar Amerika 2,500, yayin da ita Kheirandish aka ce za ta dawo birnin na Yazad domin ita ma a yi mata shari'a. Ali Zamani dai dan shekara sama da ashirin ne yayin da ita 'yar wasan ta haura shekara 50.
Kamfanin dillancin labarai na Iran (wato IRNA) ya ruwaito cewa wakilin majalisar Musulunci ta kasar baki daya a nan birnin Yazad, Malam Mohsen Talebpour, ne ya shirya zanga-zangar yin Allah-wadai da sumbar da aka yi. "A yau abokan gabarmu sun kai wa addininmu na Musulunci hari," inji shi.
Kafafen yada labarai ma sun yi tir da Ali Zamani da Gohar Kheirandish. Jaridar mako-mako mai suna Ya lessaarat cewa ta yi a cikin filin ra'ayinta, "Abokan gabarmu suna kokarin bata Musulunci ta hanyar al'adunmu kuma wannan abin da ya faru shi ne babban misalin hakan."
Shi ma wani jami'in Ma'aikatar Al'adu da ke birnin an kama shi saboda ya yi sake har mutanen biyu da ake zargi suka bar birnin da farko, ana tuhumarsa da laifin "hadin baki" da su. Shi ma daga bisani an bada belinsa a kan dalar Amerika 2,250.
Wani jami'in Ma'aikatar Al'adun kuma ya ce, "Duk da yake mun yi Allah-wadai da faruwar sumbar amma ya kamata a lura da cewa abin ya faru ne a wurin da ake ta shagali, sa'annan kuma ba wai an shirya yin hakan ba ne tun da farko."
Idan aka bi tarihi, za a taras cewa shirin fim a Iran ya sha gamuwa da wahalhalu. Hukuma tana tsaurarawa wajen tace finafinai. 'Yan fim sukan yi kokarin ganin sun shallake dokokin da aka kafa masu bisa turbar addini. A kasashen duniya finafinan Iran sukan samu kyaututtukan yabo saboda tsaruwarsu.
An dan rage matsin da akan yi wa jama'a a kasar tun lokacin da Shugaba Mohammad Khatami, wanda mai sassaucin ra'ayi ne, ya dare karagar mulkin kasar bayan an yi zabe a cikin 1997. Misali an dan sakar wa mata mara a kan yadda suke sanya tufafi idan za su unguwa, yanzu akan kauda kai idan an ga mace ta sanya janbaki da kuma takalma sandal, koda yake tilas ne mace ta rufe jikinta da hijabi daga sama har kasa. To amma sam ba a yarda mace da namiji su taba jikin juna ba, wanda hakan wani abu ne da wani jami'in kasar yake ganin bai da dadi idan ya gamu da matan kasashen Turawa. Wannan ko shi ne tsohon wakilin Iran a Majalisar Dinkn Duniya, Malam Hadi Nejad Hosseinian, wanda ya gaya wa jaridar Ya lessarat lokacin da ta yi hira da shi a kan wannan al'amarin, cewa, "A lokacin walima kobukukuwa a kasar waje, nakan rike kofin gilashi a hannu daya sannan in rike jakata a daya hannun saboda kada in yi musabiha da mace. Su matan kasashen waje ba su san ka'idojin Musulunci ba, saboda haka sai su rika jin haushi idan ba ka kama hannunsu kuka gaisa ba."
Nejad Hosseinian ya ce ya taba rubuta wasika zuwa ga shugaban kare addini a Iran, wato Ayatullahi Khameini, ya tambaye shi ko an yarda a wani lokacin idan wuri ya kure (kamar a kasar waje) mutum ya yi musabiha da mace. Amsar da aka maido masa ita ce, "A kul ka kuskura!"
Tare da rahoton Parisa Hafezi.
Kash! Amerika ta hana darakta ya halarci bikin da shirinsa ya
yi zarra