Bayan an gama daura aure, wakilinmu ya kutsa kai cikin falon uwar Balaraba, MALAMA BINTA, ya samu tattaunawa da ita a kan abin farin cikin da ya same ta wanda, Allahu Akbar!, zai kasance abin bakin ciki washegari. Ga hirar tasu:
Fim: Mama, za ki iya bayyana mana farin cikinki dangane da wannan rana ta daurin Auren Balaraba?
MALAMA BINTA: Ina matukar farin ciki sosai da sosai; a yanda Allah ya nuna mana wannan rana yanzu dai mun fita kunyar mutane.
Shin akwai wata damuwa a zuciyarki ganin cewa kun shaku da Balaraba, ga shi kuma Allah ya kawo ranar daurin aurenta za ta tafi ta bar ku?
MALAMA BINTA: E, to, akwai damuwa, tunda duk cikin yarana ba wanda na shaku da shi kamar ita. Dole ne abin ya dame ni. Rabuwana da ita gaskiya ya dame ni.
Ya za ki kwatanta sauran bukukuwan da ake yi a nan gidan?
MALAMA BINTA: Alhamdu lillahi, gaskiya a nan dai ban ga bikin da ya tara jama'a kamar haka ba. Ko duk bikin da ake yi a garin nan, ban ga bikin da ya tara mutane haka ba. Alhamdu lillahi, mun gode Allah.
Kafin wannan rana ta zo, kin taba tunanin jama'ar da za su zo daurin auren za su kai haka?
MALAMA BINTA: A'a, ban zata haka ba. Ana dai fadin cewa mutane za su taru, amma ban dauka cewa mutanen za su yi yawa haka ba.
Kina da wani sako ga jama'ar arziki da suka halarci wannan daurin auren na diyarki?
MALAMA BINTA: E, ina da sako. Na gode masu kwarai da gaske a yanda suka yi farin ciki da taruwa wajen nan. (Dariya) Ban zato ba za su yi cikowa haka. Amma na gode ma jama'a sosai da sosai. Alhamdu lillahi.
Kina da sako na musamman zuwa ga Ango da Amarya 'ya'yanku?
MALAMA BINTA: Sakona shi ne Ubangiji Allah ya ba su zaman hakuri. Kuma don Allah su yi juriya da zaman duniya. Kuma su cire kunnuwansu ga mazuga.