Free Web Hosting Provider - Web Hosting - E-commerce - High Speed Internet - Free Web Page
Search the Web

Jagorar mujallun Hausa
FITOWA TA 35   Nuwamba 2002
WASIKU


BABBAN SHAFI
MU LEKA MU GANI
TALLA
Wasiku
KU TAMBAYE SU
Duniyar Finafinai
Rahoto
Malam Zurke
Rayuwarmu
Bukukuwa
Sauran Labarai
Fitattun Taurari
Dangane Da Mu
Muhawara a Zauren YAHOO!GROUPS

Wannan wani zaure ne da aka kirkira a dandalin sadarwa na zamani, wato intanet.
An gina zauren ne a kan tsarin 'Groups' na babbar masana'antar sadarwa ta intanet da ke Amerika din nan mai suna Yahoo!
A wannan zauren namu mutane suna tattaunawa ne musamman a kan finafinan bidiyo na Hausa wadanda ake yayin su yanzu.

JE KA TA NAN


Inda za ka samu tsaffin mujallun Fim
 
Je ka
Bangon Fim ta 33. Danna nan ka gani!
Bangon Fim ta 32. Danna nan ka gani!
Bangon Fim ta 31. Dannan nan ka gani!
Bangon Fim ta 30. Danna nan ka gani!
Bangon FIM ta 29. Danna nan ka gani!
Bangon FIM ta 28. Danna nan ka gani!
Bangon FIM ta 27. Danna nan ka gani!
SABON FIM MAI FITOWA!!
Daga Mujallar FIM

KAR KA BARI A BA KA LABARI!!
Akwai shahararrun 'yan wasa a ciki!!
Tallar sabon fim din da ya fito!

NORTHERN STAR FILMS

KE GABATAR DA

GAGARABADAU Fostar fim din kenan

Shiryawa: MUJALLAR Fim

Darakta HAFIZU BELLO

Wasa: Sadiya Abdu Rano, Musbahu M. Ahmad, Sani Moda, Aliyu A. Gora, Hindatu Bashir, Isa Ja, A'isha Ibrahim, Mika'il Hassan 'Gidigo,' Baban Mulika, Shu'aibu 'Kumurci', Ashiru Bazanga, Saratu Gidado, Shehu Kano, Galin Money, d.s.

Labari/Tsarawa: Iro mamman;

Daukar Hoton Bidiyo: Yahaya Skito

BABU IRINSA!

Wasu matafiya ne Allah ya hada su tafiya a tsohuwar motar Direba Moda. Kowanensu yana da MU LEKA MU GANIn yadda ya kamata motar ta rika tafiya: wasu na kukan ana bata lokaci, wasu na cewa a rage gudu...

Can a kan hanya, yaran Gagarabadau (su Kumurci) sun tare hanya suna fashi...

Labari ne na soyayya, ban dariya, tada jijiyar wuya, da ban tsoro...

Idan har ka kalli fim din ba ka yi dariya ko ka ji taraddadin sharrin basawan Gagarabadau ba, to za mu biya ka kudinka! Ka tuntube mu ta e-mail dinmu don ka samu naka

 


In kana son mu aika maka duk lokacin da muka canza shafin nan
    
   Za mu rike sirri  

by ChangeDetection

Wasikun masu karatu

GYARA KAN MAGANAR MAI H.R.B

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DON Allah ina son a dan sam mani fili cikin wannan mujallar mai farin jini domin in yi tsokaci game da mutumin da muke ganin yana daya daga cikin masu hikima da basira da kuma fasaha, ga finafinansa babu na banza. A duk lokacin da aka ce ga fim daga kamfanin H.R.B. to babu wani tababa, za ka saye shi kanka tsaye, don ka san babu shirme a ciki kuma ba ka yi asarar 'yan dari biyunka da hamsin ba. To amma sai na sha mamaki, da Rabi'u Ibrahim yake alfaharin cewa wai shi ba ya hira da 'yan jarida. Amsar da ya ba ku kan wata tambaya a Fim ta watan Satumba ta ban mamaki, kuma ya ba ni haushi. Saboda sai na ga ai wadanda suka fi shi ma suna yin hira da 'yan jarida. Don kuwa ana hira da malamai, magada annabawa. Kuma mu ba mu san aibin hira da 'yan jarida ba.

Gaskiya ni da ina ganin Harabs kamar wayayye. To ya sani cewa rashin hirarsa da 'yan jarida ba zai hana mutane fadin albarkacin bakin su game da shi ko finafinansa ba. Ni wallahi rashin sanin muhimmancin 'yan jarida da wasu 'yan fim suke yi yana ba ni mamaki. Ina son in tambayi Rabi'u idan ba ya son ka-ce-na-ce (controversy) me ya kai shi shiga harkar fim? Ina shaida mashi cewar mun ga farkon yadda Amintab Bacchan da 'yan mujallar Stardust suka kare. Saboda haka mu a nan duk wani mai fuffuka ya ce wai shi bai shiri da 'yan jarida, ko kuma shi ya fi karfin 'yan jarida, kallonsa kawai muke yi. Domin dan jarida kusan shi ne kashin bayan rayuwar al'umma, musammman ma ku 'yan fim da dole sai da 'yan jarida kuke yin wani tasiri ga al'umma. Don kuwa su suke tallata ku duniya ta san ku, kuma ma wasu da kudinsu suke neman 'yan jarida ido rufe don dai kawai su bayyana wa duniya manufofinsu.

Hajiya Ladidi Yusuf (Mrs. Addulwahab),

No. A.K. 1, Sallau Road, Badikko, Kaduna.

FINAFINAN HRB SUNA DA MA'ANA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA rubuto wannan wasika ne domin in yaba wa shahararren kamfanin nan 'H.R.B. Production' a bisa kokarin da yake yi na na shirya nishadantarwa. Bayan haka kamfanin yana kokarin zabo shahararrarun 'yan wasa da suka kware. Mai karatu na iya yarda da haka idan ya kalli finafinan da kamfanin ya shirya. Saboda haka wannan kamfani ya cancanci yabo musamman saboda kyakkyawar gudunmawar da yake bayarwa a sha'anin mantar da amana.

Ina gaida 'yan wasa kamar su Ibrahim Maishunku, Ali Nuhu, Aminu Acid, Alasan Kwalle, Aminu A. Shariff (Momo), Kumurci, Sani Danja, Shu'aibu Lilisco, Sani Mai Iska, Tijjani Ibraheem da kuma Hafizu Bello.

Suleiman Musa Bodinga,

Shop No. F20, Sokoto Central Market, P.O. Box 36, Bodinga, L.G.A., Jihar Sokoto.

SALIHA TANA BURGE NI

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DA farko ina yi wa Shu'aibu Lawan ta'aziyyar matarsa Balaraba Mohammed. Allah ya jikanta. Ina mika gaisuwata ga A'isha Ibrahim (Saliha). Finafinanta suna burge ni. Na gode.

Abou-Rashid Idris,

Yalwa Road, Talatan Mafara, Jihar Zamfara O63 - 75094.

NA JI DADIN HIRAR NANA LILI

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA son in sanar da ku cewa na ji dadin mujallarku ta watan Satumba, domin na ga abin da na dade ina nema, wato hira da Nana Lili Katsina. A gaskiya na dade ina kaunarta. Ban kuma san ta ba sai sunanta nake ji. Amma ta shiga raina matuka. Don haka wannan hira sai na ga kamar don ni kadai kuka yi ta. Allah ya ja zamanin mujallar Fim. Sa'annan kuma ina son in ba da shawara cewar, zanen da kuka yi na 'yan fim suna dambe wallahi ya dauki hankalina. Ya kamata a dan rika sanya mana zane (cartoon) jefi-jefi a cikin mujallar don kuwa yana da kayatarwa. Gaskiya ina cikin halin rashin lafiya amma wallahi karanta labarin nan ya sanya ni nishadi da cin dariya har ina kwalla. Dubi wai don Allah don Annabi duk irin yadda Hindatu Bashir ke da aji amma ta tsaya fada da wadda ma 'yan kallo ba su sani ba? Don Allah don Annabi su daina ba mu kunya. Suna zubar da ajinsu a aikin banza domin kuwa sun san mazan nan ba aurensu za su yi ba amma su dinga ba hammata iska. Haba! Ya kamata su yi wa kansu fada.

Hajiya Habiba Yusuf Abdulwahab,

No. A.K.1, Sallau Road, Badikko, Kaduna.

ALLAH YA ZAUNAR DA SALIHA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA taya A'isha Ibrahim murnar yin aurenta, ina rokon Allah ya ba da zaman lafiya, kuma ya ba da zuri'a tagari, amin. A karshe ina mika sakon gaisuwa ga babban edita da ma'aikatansa.

Bello Agwada mai kanwa,

Bakin Kasuwar Yauri, P.O. Box 78, Yauri, Yelwa-Yauri, Jihar Kebbi.

MU SHAKATA YA YI, TO AMMA...

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA rubuto wannan takarda domin nuna matukar farin cikina game da shirye-shirye da kamfanin 'Mandawari Enterprises' ke yi na Mu Shakata 3&4. A gaskiya sun burge ni. Sai dai wani dan tsokaci da nake son yi game da shirin Mu Shakata 3 a kan wata waka da wasu daga cikin 'yan wasan Kano su 12 suka yi wadda na ji shugaban shirin ya kira da "taurarin Kano 12". Na yi matukar mamakin rashin ganin gwanayena, wato Abida Mohammed da Hauwa Ali Dodo.

A Mu Shakata 4 kuwa abin da ya ba ni mamaki shi ne wurin da Halima Adamu Yahaya ta yi hira da wasu masoya guda biyu. Ko ba komai mu mata an san mu da kunya da kawaici, to amma sai na ga ita macen da an yi mata wasu tambayoyi game da masoyin nata sai ta bayyana ra'ayinta game da shi, amma shi namijin har aka yi aka gama ban ji inda aka yi masa ko da tambaya daya da ta shafi masoyiyar tasa ba. Ni a ganina namiji ya dace a yi ma irin tambayoyin da aka yi mata, amma ba mace ba. In ko har ba za a iya tambayar namiji ba ta yaya ita macen za a tambaye ta? 'Yan jaridar asali ba haka suke aiwatar da aikinsu ba! Da fatan za a samu gyara a gaba .

Gaisuwa ta musamman ga Abida Mohammed, Biba, SaimaMohammed, Hadiza Kabara, Fati Baffa Fagge, Aina'u Ade, Saratu Gidado, Hajjo, Shu'aibu Lilisco, Misbahu Ahmad, Ahmad Nuhu, Ali Nuhu, Nura Hussaini, Aminu Dambazau da kuma Ibrahim Mohammed Mandawari.

Binta Tukur (Ta'alhazai),

No. 56, Galadima Dudi Road, Kofar Fada Malumfashi, Jihar Katsina.

FIM TANA KARA BA SU TAZARA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

ABIN nan da Hausawa ke cewa "su wane ko wance an wuce tsara" to ina son in dan yi tsokaci a nan. Idan ba ku sani ba to ku sani, idan kun sani kuma to matashiya ce. Ita fa mujallar Fim tun da ma can ba tsararsu ba ce, tun asali ita ce kan gaba ballantana a ce wai "ta wuce tsara" tun fil-azal da ma ba tare suka taso ba, kuma sun sani cewar tun shekaranjiya zuwa jiya, kawo izuwa yau, har magajin gobe Fim ita ke kan gaba, kuma tana ta kara ba su tazara wadda ba ta misaltuwa. Ita za ta kuma ci gaba da jagoranci har sa'ad da Mahadi zai bayyana. Mujallar ta samu karbuwa dari bisa dari ga jama'ar kasar nan har da kasashen ketare. Na gaba ya riga fa ya yi gaba.

Muna fatan Allah ya ja zamanin mujallar Fim da duk ma'aikatanta maza da mata.

Adda'u Mohammad Sani Bakori

No. 37 Tafoki Road, Faskari, Faskari L.G.A., Jihar Katsina.

MUJALLAR FIM CE A GABA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA rubuto wannan wasika ne domin in bayyana jin dadi tare da gamsuwa da irin ayyukan da wannan mujallar take yi, musamman wajen bayar da labarai na gaskiya babu kari, da ilimantarwa tare da nishadantarwa. Fim ita ce ta farko a nan Arewa wajen bunkasa, farin jini, kyawun tsari da inganci. Na jinjina mata bisa irin kokarin da take yi wajen inganta harkar fim a Arewa.

A gaskiya mujallar ta zame mani abokiyar hira a duk lokacin da nake bukatar haka kuma gare ta nake samun karin ilimi dangane da harkar fim da ma rayuwar duniya gaba daya.

Daga karshe nake mika gaisuwa ta musamman ga wadannan jarumai: Ali Nuhu, Hadiza Kabara, Kabiru Maikaba, Hajara Usman, Hauwa Ali Dodo, da Zulkilu Muhammad.

Abubakar Alhaji Adam Baga,

Finance Department, Kukawa LGA, Jihar Borno.

GAISUWA A GARE KU

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DALILIN wannan wasika shi ne domin in sar da sakon gaisuwa ga ma'aikatan wannan mujallar. Domin a gaskiya ina jin dadin karanta ta shi ya sa na ga ya dace in yi wannan wasika domin in jinjina maku.

Sharhabilu Isa,

Abarshi Secondary School, Yelwa Yauri, P.O. Box 100 Yauri, Jihar Kebbi.

KURAKURAI CIKIN BURIN ZUCIYA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DALILIN wannan wasika shi ne na kalli Burin Zuciya na ga gyara a ciki, na ga ya dace in yi wa furodusan gyara, wato Ibrahim Mohammed Mandawari. Gyara na farko shi ne na farko sun nuna cewa Sarki Abdurrahman ya bai wa Gimbiya kyautar bayi; na biyu shi ne wurin da shi Mandawari ya ba Gimbiya tarihinshi, ka ga wannan tarihin rayuwarsa bai nuna inda ya fito ba; na uku, Gimbiya ta ji wakarshi san da aka fitar da shi gari aka kai shi daji dogarai suka doke shi, da ya farfado sai ya fara waka, da ta ji wakar sai ta fita ta gudu, sai ga ta a garin Sarki Abdurrahman. Idan za a tuna, da farko sun ce Sarki Abdurrahman ya aiko mata bayi amma da ta yi batan kai sai garin Sarki Abdurrahman amma ya ce bai san ta ba! Kuma ga shi sun ce Mandawari na cikin bayin da Sarki Abdurrahman ya aika mata da su. Sannan ga shi shi ma Mandawari ya zo garin Sarki Abdurrahman inda shike a da can. Amma da ya zo ba wanda ya san shi.

Daga karshe ina mai sauraron Mandawari. Kuma ya ce shi ne 'baban soyayya.' To baban soyayya ka yi nazari mana.

Hamza Adamu mai saida 'yan kunne,

Bakin kasuwar Yauri, P. O. Box 78, Yauri, Jihar Kebbi.

GYARA A FIM DIN BURI

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA mika sakon gaisuwa da jinjinawa zuwa ga dukkan jami'an wannan mashahurin kamfani, watau mujallar Fim, a kan kokarin da suke yi na fahimtar da jama'a da kuma samar da labarai a kan harkokin fim. Bayan haka, zan yi amfani da wannan dama in gabatar da wata kasida a kan fim din Buri da na kalla.

A gaskiya Buri ya kayatar da ni, kasancewar abubuwan da yake karantarwa suna faruwa. Sai dai kash! Ni a wurin wannan fim ya samu rabuwar Albinla kuma daga wurin mutum guda, wato jarumin wannan fim Alhaji Hamisu Iyan-Tama a inda a rayuwarsa ta duniyar farko kamar yanda ake ba da labari ya kasance yana karantarwa ne, wanda cikin ikon Allah ya samu karin girma. To a gaskiya kamata ya yi ya ci gaba da kasancewa malami ko da ko zai kasance shi ne shugaban makaranta, idan kuma ya bar harkar malanta ne to kamata ya yi a nuna wa mutane, don babu malamin da ke barin makarantar da yake karantarwa ya koma kasashen waje a kan harkar kasuwanci kuma kasaitaccen da ba ma za a taba hada shi da wancan tsohon malami ba. To wannan shi ne kuskuren da na fahimta a fim din.

Suleiman Attahiru Gusau,

Gusau Hotel Limited, Zaria Road, PMB 1093, Gusau, Jihar Zamfara. Tel: Office 063 200396 - 200727

HAR AN FARA NUNA TSIRAICI!

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

MUNA so mu fadakar da wasu 'yan fim da suka dauki akidar nuna yara tsirara a fim. Mun ga haka a finafinai kamar darasi, Mariyatu, da kuma Tangaran 2. Wannan ai jahilci ne da kuma wai da sunan fadakarwa. Babu addinin da ya yarda a nuna tsiraici ballantana kuma addinin Musulunci.

Daga karshe muna gaida Yakubu Muhammad, Ibrahim Sheme, Mandawari, Maishunku, Ahmad, Ali, da kuma Ishaq Sidi Ishaq.

A'isha Bello Sadiq, Amina Isa Sheshe da Jamila Abubakar,

B.U.K. Staff Secondary School, B.U.K., Kano.

MUNA CIN MORIYAR MUJALLA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA mai mika gaisuwa ga masoyana kamar su Ibrahim Sheme, Alhaji Garba Dangida, Ashafa Murnai Barkiya da sauran ma'aikatansu, ganin yadda kuke namijin kokarin aikin wasikunmu. Sannan kuma muna cin amfanin mujalla sosai, tana wayar mana da kai a kan abin da ba mu sani ba.

Alhaji Sama'ila Lawal Kwashi Jibia,

Hamalu Vedio & CD Disc Centre, No. 2 Mamman Zugau Road, Jibia, Jihar Katsina.

NASIHA KAN MATA MASU GUDOWA

ZUWA GA 'YAN FIM,

KAMAR yadda muka san aikinku shi ne ilimantarwa tare da tarbiyyantarwa, saboda haka duk 'yar wasan da kuka sami labarin cewa gudowa ta yi daga gidan iyayenta ba tare da son ransu ba, don Allah ku da kuke a matsayin abokan sana arta ku yi mata nasiha ta koma ga iyayenta, idan kuna neman albarka a cikin sana'arku. Ku yi irin na marigayiya Balaraba, Allah ya jikanta ta da rahamarsa. Domin ita ba ta shiga wannan harka ta fim ba sai da izinin iyayenta. aboda haka duk wadda kuka yi wa nasiha idan ta ki komawa gida sai ku kore ta kawai tunda ku kuna da mutuncinku. Amma idan ba haka ba yara suna shiga duniya suna lalacewa a sanadiyyarku. Wadansu kuma suna kashe aurensu. Mu mun riga mun san niyyarku ta alheri ce.

Nasiru Sabo,

No. 17, Anguwar Malamai, T/Wada, Zariya, Jihar Kaduna.

A KARRAMA 'YAN MUJALAR FIM

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DALILIN rubuto wannan takarda shi ne domin in yi jinjina ga mawallafin wannan mujallar, watau Malam Ibrahim Sheme, a kan namijin kokarin da yake yi na ciyar da harshen Hausa da Hausawa gaba a duk duniya.

Sannan kuma ina fatan yadda mujallar ta karrama su Alee Baba Yakasai, to a wannan shekarar sai ta karrama ma'aikatanta irin su Ashafa, Aliyu A. Gora II, Ibro Mammam, Sadiya Abdu Rano, Bashir Yahuza, da sauransu.

Gaisuwa mai yawa ga Furofesa Abdalla Uba Adamu da kuma 'yan wasa irin su Ali Nuhu, Ahmed S. Nuhu, Abida, Hindatu, Momo, Sir Hafizu Bello, Yakubu Lere, Tijjani Ibraheem, Tsigai, Zik, Bashir Nayaya, da Sani Garba S.K. (Suya).

Safiyanu Ibrahim Musawa,

c/o Mani Ibrahim Musawa, Gen. Hospital, Katsina, PMB 2918 Katsina. YABO GA CIBIYAR HAUSA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA roko ku dan ba ni fili in mika sakon gaisuwata da nuna farin cikina a kan taron da Cibiyar Nazarin Hausa ta Jami'ar Usmanu Danfodiyo ta Sokoto ta shirya kuma kuka ba da labarinsa a Fim ta Satumba. Cibiyar ta gayyato manyan malamai masana harshen Hausa da malaman addini, 'yan wasan finafinai, da dai sauransu. Wallahi wannan cibiya ta yi abin yabo kuma ya kamata a yaba mata, domin a gaskiya yanzu ne na san cewa muna da iyaye a nan Arewa.

Sannan wajen fannin mata kuwa a gaskiya a duba yadda suke sanya suturarsu da kuma yadda suke barin kansu a bude kamar 'ya'yan arna. Nan ma akwai gyara. Kuma wajen yawaita soyayya nan ma a yi gyara don gaskiya ya kamata a fi kwadaita wa masoya yadda za su yi aure a tsari irin yadda Musulunci ya shimfida.

Daga karshe ina son in mika gaisuwa ga shugabanmu na kungiyar wasan kwaikwaiyo da taimakon kai da kai ta Kabala Costain, Alhaji Saminu M. Mahmoud, da Yusuf Barau, Sani Moda, Hauwa Ali Dodo, Wasila Isma'il, Ali Nuhu, Ahmed S. Nuhu, Ibrahim Mandawari, Shu'aibu Lawan, daraktoci da kuma furodusoshi gaba daya.

Aminu Gidado Kaduna,

Fed. Min. of Works & Housing,

Field Headquaters, Lafia, P.M.B. 43, Jihar Nassarawa.

... KU YI AIKI DA SHAWARWARIN

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DON Allah ku ba ni fili a cikin mujalla mai farin jini domin in bayar da shawara ga furodusoshi da daraktaci. Don Allah su yi kokari su nemi 'yan'uwansu da suka samu halartar taron da aka gudanar a Jami'ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato, a kan "Sabon salon tafiyar Adabin Hausa: Ci-gaba ko Ci-baya?"

A gaskiya an gabatar da kasidu da shawarwari masu ma'ana da kuma gamsarwa, wadanda za su gyara harkar fim da kuma kyautata al'ada da addinin Bahaushe. Ina ba su shawara da cewa su yi hakuri, su jure, su yi amfani da wadannan kasidu, kada su yi kwadayin riba da kuma dan abin duniyar da za su samu, su yi dubi kan kiyaye hakkin Musulunci da Musulmi, domin Ubangiji zai saka wa kowa kan abin da ya aikata.

Abdul Mumin Abdul Fatah,

Anguwar Malam Dahiru, Gidan Limamin Jumma'a, Suleja, Jihar Neja.

TIJJANI IBRAHEEM BAI DA LAIFI

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA so in yi amfani wannan damar in yi magana a kan wani mai karatunku Nasiru Attahiru Gusau, wanda wai yake so ya ba darakta Tijjani Ibraheem shawara a kan martanin da ya mayar wa Halima Adamu Yahaya babu wata maganar "yabon kai jahilci" yara nawa ya nema ai bai taba fada ba, ita ma kamawa ta yi. In an yi maka abin kirki bai kamata ya bar ta a ransa ba. Laifi ta yi. Don an yi mata fada ai ba wani abu ba ne, gyara mata kuskure ya yi a matsayinsa na babba.

Kuma ina so in kara game tabbatar da maganar da Tijjani Ibraheem ya yi game da gulmace-gulmacen da ake a kan su Ali Nuhu; to ai yabon gwani ya zama dole, Ali ya zama ciwon ido, babu yadda za a yi da shi sai hakuri, kuma wanda ya dace ai da shi za a yi kyau da biyayya. Ina masu fatan alkhairi, Allah ya kara dankon zumunci, Allah ya sa su dade suna yi. Gaisuwa ga babban baba Tijjani Ibraheem.

Fauziyya I. Sheshe,

Faculty of Law, Bayero University, Kano.

WA KE RUBUTA FILIN M. ZURKE?

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA rubuto maku wannan wasika ne don in tambaye ku wani abu da yake daure mani da kai. Ni dai kowane wata idan mujallarku ta fito, idan ina da zarafi ba ta wuce ni, kuma da zaran na saya na barke ledar filin Malam Zurke nake karantawa kafin in karanta kowane labari.

To tambayata a nan ita ce don Allah wa ke rubuta wannan fili; ko wanene ba karamin ilimi gare shi ba. Ina fatan za ku share ma masu karanta filin hawaye da wannan tambaya tawa.

Daga karshe ina fatan za ku isar mani da gaisuwata zuwa ga Ibrahim Maishunku, Sanusi Burhan, Aina'u Ade, Ishaq Sidi Ishaq, Yakubu Muhammad, Sani Danja da kuma Hamisu Iyan-Tama.

Hajiya Hannatu Ibrahim Omar,

Emir's Palace, Kaltungo, Jihar Gombe.

Hajiya, filin Malam Zurke fili ne na nuni-cikin-nishadi, kuma Malam Zurke ya ce a gaya maki cewa shi ne yake rubuta filinsa!

ALLAH YA JIKAN MASOYIYATA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA son ku isar mani da ta'aziyyata dangane da rasuwar babbar masoyiyata, kuma matar Shu'aibu Lawan Kumurci, wato Balaraba. Allah ya jikanta, ya sa aljanna ce makomarta, ya yi ma Shu'aibu zabi na alheri.

A karshe, ina mika gaisuwata ga Ali Nuhu, Ahmad S. Nuhu, Ibrahim Mandawari, Hajara Usman, Hadiza Kabara, da Maryam Aliyu. Wassalam.

Hauwa'u Sani Faskari,

c/o Sani Umar Faskari, Rural Electrification Board, Musawa, Jihar Katsina.

IBRO KA DAINA CIKA BAKI

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DON Allah ku taimaka ku isar mini da sako zuwa ga shahararren dan wasan nan Rabilu Musa (Ibro). Ina so ya daina cika baki cewa babu wanda ya isa ya yi wani abu a duniya da zai ba shi tsoro ko kuma babu wani mutum da zai yi masa wani abu. Ni ina daga cikin masu son shirin Ibro. Ibro, ka tuna fa duniya ba ta son mutum mai cika baki. Don Allah ka rika tunani. Bayan haka inason ku mika gaisuwata ga Shu'aibu Lawan Kumurci, Hadiza Kabara, Sani Garba S.K., Ibrahim Sheme da Ashafa Murnai Barkiya.

Yayani Popular Guy Isawa, P.O.Box 279 Isawa, Giade L.G.A., Jihar Bauchi.

MUN GA WULAKANCI A GUN IBRO

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DON Allah ina son ku yi mani kokarin tambayar mani Ibro game da wani abin mamakin da ya yi a lokacin da ya zo Kwantagora. Wannan abin na gani da idona, ba labari aka ba ni ba, wanda idan da labari aka ba ni, sai in karyata zancen. To a ranar 7 ga watan Agusta Ibro na garin Kwantagora tare da tawagarsa, mun je masaukinsu don mu ganar ma idonmu. Har ma mun gaisa da Tsigai, Cinnaka da sauransu, sai ba mu ga Ibro da Kulu ba. Muka tambaya aka ce suna baya suna wani wasa. Sai muka je kallo. Me zai faru? Ai haka na ga sun sami bulalarsu ta danyen haki wadda muke kira "miyar tsanya", suka yi ta zabgar mutane har wasu na faduwa. Ai ko da na ga haka sai muka yi gaba kar mu ji ciwo a banza.

Sai na ga dai shi Ibro farin jini ne da son da jama'a ke masa ya sa har wasu suka aje ayyukansu suka nufi wurinsa, amma ya yi ta wulakanta mutane. To shi ne ban gane ba: wannan duk a cikin wasa ne ko kuwa ya yi don ya wulakanta mutane ne? To idan ko haka ne gaskiya bai kyauta ba. Ya tuna fa, ba shi kadai ne dan wasan da ya fara zuwa Kwantagora ba; Tahir Fage da jama'arsa sun zo, sannan kuma tun kafin a san wani wai Ibro Golobo ya zo da nasa jama'ar amma ba wanda na ga ya yi ma jama'a irin abin da Ibro ya yi. Saboda haka nake ba shi shawara da ya daina, jama'a ma ai rahama ne.

Malama Fatima Mohammed Ciroma (Mrs Abubakar),

Rimaye Primary School, Kontagora, Jihar Neja.

LAIFIN ME NA YI MAKU?

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DON Allah ina so ku ba ni fili cikin wannan mujallar mai farin jini domin in tambaye ku ce war shin wasikata tana zuwa ko ba ku bukatar in rika rubutowa? Na jima ina rubuto wasiku ban ga alamun kun same su ba.

Daga karshe ina mai mika gaisuwa ta ga jaruma Aina'u Ade.

Abubakar Garba Jibia,

No 3, Mamman Zugau Road, Jibia, Jihar Katsina.

Abubakar, ka binciki hanyar da kake aiko da wasikunka. Da mun same su, da ka ga mun buga.

SHAWARA GA MIJIN A'ISHA MUSA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA rubuto wannan wasikar ne domin in nuna murna da farin ciki da auren Malama A'isha Musa da Malam Ali Nayara.

Shawara ga Malam Ali Nayara ita ce don Allah ka rike matarka ka kuma lura da yadda aka yi wannan aure, kada ka ba mu kunya.

Da kuma fatan Allah ya ba da zaman lafiya da hakuri, amin.

Ramalan A. Ahmed, Abuja. Ahmed S. Nuhu da Maryam Aliyu: An fasa auren!

WANI labari da muka samu da dumi-duminsa ya nuna cewa danyar soyayyar nan tsakanin Ahmad S. Nuhu da Maryam Aliyu (Mushaqqa) yanzu ta kare. Majiya mai tushe ta tabbatar mana da cewa Ahmed ya fasa auren Ba'abziniyar yarinyar bayan an dade ana ce-ce-ku-ce da zarge-zarge. Yayin da wasu 'yan fim suke zargin Ali Nuhu da kawo karshen soyayyar, wani abokinsa na kut da kut ya ce, "Ba ruwan Ali. Ahmed ne da kansa ya janye."

Wani mai lura da al'amuran industiri kuma ya ce, "Kai rabu da su! Ahmed ya yi sabuwar budurwa ne, karamar yarinya 'yar jika-jika, shi ya sa ya juya wa Maryam baya."

Fim ta san cewa tuni Ahmed ya yi niyyar auren Maryam, domin har kayan auren ya saisaya. Fasawar da ya yi ta girgiza Maryam da iyayenta, inji majiyarmu, har lissafinsu ya dagula. "Ka ga yanzu ai sai ta nemi daidai da ita," inji wata 'yar wasa da ta tofa albarkacin bakinta a kan wannan al'amarin.

NA JI DADINKU A INTANET

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

ASSALAMU alaikum! Na ji dadi kwarai da nake karanta mujallarku a intanet. Allah shi taimake ku, amin.

Kamaluddeen Dahiru

29 Rabah Road Kaduna, P.O. Box 5010, Kaduna.

FATI MOH'D LOKACI YA YI...

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA so in yi amfani da wannan dama taya gwanata Fati Mohammed (Mrs. Mai Iska) murnar abin alhairin da ya same ta. Muna mata fatan Allah ya kara daukaka ta, ya sa ta fi haka. Ina kuma son in ba ta shawara a kan yanzu lokaci ya yi da za ta koma makaranta ta yi ilimi mai zurfi, yadda duk inda za ta je a duniyar nan ba za ta sami matsala ba. Kuma za ta samu daukaka da girma fiye da yanzu, cikin yardar Ubangiji. Ina kuma so fati ta dada yin hakuri da mutane masu ziyartarta; ta tuna ba ita ta kai kanta wannan matsayin ba, saboda haka ta rinka bin mutane a sannu.

A karshe gaisuwata ga Hadiza Kabara, babban yaya Ibrahim Mandawari, Hajara Usman , da Hajiya Amina Garba. Allah ya kara fahimta, amin summa amin.

Maimuna Bello (Mrs. Bello)

KUNA CIKA AIKINKU

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

BAYAN gaysua da fatan alhéri, ina gaîda Aina'u Adé da duka jamma'a Mujallar fim. Ina mai godiya ga Allah da ya kawo mu wannan lokacin. Gaskiya ina jin dadin rahotannin da kuke yi a kan finafinan Hausa. Mujallar tana cika aikinta kuma tana taimaka wa jama'a su fahimci ma'anar fim. A karshe zan mika gaisuwata ga dukkan 'yn wasan fim na hausa. Ina so ku ba ni adireshin Sadiya Abdu Rano.

Ina meka gaysua ta'asia ga duka masu wasan Hausa.

Maman Yawale,

Reprogaphe, National Assembly of Niger, P.O. Box 12234 Niamey, Niger Republic

TSOKACI KAN GAGARABADAU

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

TUN lokacin da tallar fim din Gagarabadau ta fito na sa ido kan fitowarsa. Lallai kun nuna kokari sai a kara zage damtse domin sauran finafinanku masu fitowa nan gaba. Sai dai matsala ta ita ce shin ba ku ne ke sukar waka da raye-raye ba? Kuma na lura wakar da Laraba (Sadiya Abdu Rano) ta yi wa shi Gagarabadau ta so ta yi kama da wata waka da aka yi a cikn wani fim na Indiya mai suna Tridev. Saboda haka ina neman karin bayani game da wa nnan .

A gaida Ashafa da baba Ibrahim Sheme.Wassalam.

Kasim Lawal Ibrahim,

P.O. Box 75, Kaura Namoda, Jihar Zamfara.

Malam Kasim, a gaskiya ba mu ne muke sukar waka da rawa a fim ba kamar yadda kake tsammani; wasu masu karatunmu ne. Kuma muna ba kowa dama ya fadi abin da ya ga dama a cikin hankali. Sa'annan batun waka ta yi kama da ta cikin Tridev, wannan gaskiya ne. Amma ba ita din ce muka kwafo muka maida ita ta Hausa ba, arashi ne kurum. Kuma kar ka manta, ai kusan kowace waka a duniyar nan za ta iya yin kama da wata wakar a wani yaren ko wata nahiyar, sai dai in ba a bincika ba. Ita wakar Tridev da kake cewa ai ainihi wakar wata zabiyar Amerika ce mai suna Gloria Estefan, wadda ke da rundunar kida mai suna "Miami Sound Machine', suka kwafa suka yi. A cikin faifan ita Estefan mai suna "Evolution" wakar take. Haka kuma ka fadi sunan kowace waka, mu kuma za mu ba ka sunan wata da suka yi kama a wajen kida ko kari, ciki kuwa har da wakokin Shata, Dankwairo ko Maidaji Sabonbirni! Mun gode.

INA AINA'U ADE?

ZUWA GA KUNGIYAR MASU SHIRYA FINAFINAI TA JIHAR KANO,

NA rubuto maku wannan wasika damin in ji yadda harkokin fim ke gudana. Da yake mun tura maku wasiku kuma ba wani karin bayani. Wanda yake idan ba ta wannan hanya ba ba yadda za a yi mu sa mu damar tuntubarku. Idan za ka iya tunawa, lokacin da muka rubuto maku waccen wasika, mun gaya maku cewa ta hanyar (intanet ce kawai muke jin labarinku a yanar mujallar Fim (www.fim.tvheavencom).

Ga sakona ku isar mani ga Aina'u Ade cewa ta ba ni adireshinta na i-mel domin mu samu hanyar yin hulda a tsakaninmu. Kuma ina fatan ba za a samu tsaiko ba saboda a gaskiya ba na ji dadin a ce ba wani bayani. Ina fatan wannan ba za ta wuce kwana daya ba ko biyu. Na gode.

Almustapha Sidi,

Varna Medical University, Bulgaria

KADA MANDAWARI YA BIYE MASU

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA karanta takardar da Ibrahim Sheme ya yi game da Mandawari mai take "Tsakanin Mandawari , Anabawa da Sahabbai". Yadda Sheme ya yi, ya yi daidai kuma wannan ya nuna mana bambancin da ke tsakanin 'yan jarida da 'yan wasan kwaikwayo. Da a ce 'yan fim ne za su maida martani da mutum ba zai iya karanta abin ba saboda bakaken maganganun da za su sa a ciki; amma Sheme ya bi abin cikin fahimata da dattijantaka. Sabod haka don Allah 'yan fim ga abin koyi nan. Sannan ina so in roki Mandawari da kar ya biye wa wadanda ba su san an shiga sabon karni ba. 'Yan fim kuma ina so su san da mujallar Fim suke rawa saboda haka kalubalensu!

Maimuna Bello (Mrs. Bello)

M.Z. FARU YA YI WA MAJE SATA?

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

KAI tsaye nake son sanar da shugaban Kungiyar Furodusoshi ta Jihar Sokoto, M.Z. Faru, cewar ya yi abin kunya, musanman satar fasaha rana tsaka da ya yi a fim dinsa mai suna Baiwa. Sanin kowa ne an dauko wannan labari ne daga littafin shahararren marubucin nan, yaro mai farin jini Maje El-Hajeej Hotoro mai suna Gidan Kashe Ahu. Labari ne na wata yarinya mai suna Nabila wacce duk wanda ta aura mutuwa yake yi, har sai da ta yi aure sau uku mazan suna mutuwa. Daga karshe wani saurayi mai suna Salahuddeen ya dage sai ya aure ta.

M.Z. Faru, zan so sanin hujjar da za ka bai wa makaranta littattafansa na cewar kai ba satar fasaharsa ka yi ba? A gaskiya ka yi faduwar bakar tasa! Kuma saboda rashin fasaha irin taka sai ka sa wa fim din sunan marubucin, wato lakanin da ake yi masa a mujalla: " Dan Baiwa". Ka sani cewa fim din ba zai yi kasuwa ba, don zaluncin da ka yi. Da a ce Majen ka samu kuka daidaita, da fim din ya yi farin jini. Ko ba ka da labarin daukakar da mawallafin yake da ita ne? Ka bincika nan garin da kake ka sha labari. Ka kuma kara bincikawa kai yadda aka matsu da fitowar fim din Juyayi da Ruhi albarkacin sunansa.

Rukayya A.A. Lamido Buhari

No. 120, Taiwo Avenue, Sango-Otta, Jihar Ogun.

'YAN MATA KU DAINA RAWA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA gode maku kan yadda kuke wayar da kan jama'a a kan harkokin fim din Hausa da na Indiya da na Amerika. Abu na biyu shi ne ina nuna bakin cikina dan gane da yadda wasu 'yan matan fim suke yin wasa har suke kokarin nuna ma duniya cewa sun tashi daga fadakarwa sun koma lalatarwa, misali yadda suke raye-raye suna cin zarafin addini da al'adarmu wanda yake komi ta dade za su mutu su hadu da Allah, idan ba su tuba ba su hadu da azabarsa. Ina kira da su ji tsoron Allah su bari. Su tuna akwai tsufa kuma akwai haifuwa kuma duk abin da mutum ya shuka shi zai girba. Allah ya shirya mu baki daya.

Sidi S. Ibrahim

Kofar Atiku, Ubandoma Road, Sokoto.

SAURAN MU GA DAREN FARKO

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA rubuto maku wannan takarda domin in yi jinjina gare ku kasancewar kuna fadakar da jama'a. Allah shi taimake ku shi kara daukaka wannan mujalla da mutanenta, amin. Bayan haka ina kara jinjina da yabo ga furodusa da kuma darakta na Gagarabadau. Hakika an sanya basira da hikima a ciki. Muna jiran fitowar na gaba, watau Daren Farko.

Gaisuwa ga Ibrahim Sheme, Fati Baffa Fagge, Zahara'u Shata, Ibrahim Maishunku, sannan shugaban matasa masu fim din Hausa Ali Nuhu. Na gode.

Babagida Muh'd B.

IBB Provision Store, Shop No. 4, Ubandoma Road, Sokoto.

NI MA NA SHIGO CIKIN JAMA'A

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA farin cikin sanar da ku cewa to yau ni ma na bi sahun 'yan'uwa, domin na bude i-mel domin saduwa da ku a kai a kai. Ina fata za mu amfani juna da wannan. Na gode.

Ilyasu Abdulmumini (Tantiri)

Furodusa, darakta kuma dan wasa

SHAWARA GA BASHIR NAYAYA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA so a mika min sakon gaisuwa ga gwanina Bashir Nayaya. Wallahi Uncle Bashir kana matukar burge ni a duk fim din da ka fito. Amma don Allah kar ka kara yin wasa mai kama da wanda ka yi a Sai A Lahira ko nawa za a biya ka. Uncle Bashir ba na son sunanka ya baci a wajen jama'a.

Amina Sulaiman Gombe

KUMURCI KA YI NAZARI TUKUNA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DALILIN rubuto maku wannan wasika shi ne domin in yaba maku, in nuna maku farin cikina da jin dadi game da wasikata ta farko da na aika maku kuma ta samu buguwa a cikin watan Satumba tare da amsa tambayar da na yi. Ina so ku taimaka mani da mujallar da aka bayar da tarihin Ciroki ta adireshina.

A karshe ina so ku mika shawarata zuwa ga Shu'aibu Kumurci da ya yi nazari matukar gase game da so da yake yi wa Maryam Umar kafin ya kai shi ga zancen aure. Allah ya sa Balaraba ta huta, ya sa kabari ya zama wurin aminci ne a gare ta, mu kuma ya sa mu cika da imani. Don Allah ku isar mani da ta' aziyyata ga Kumarci da iyalan marigayiya Balaraba.

Da fatan Allah shi kara wa mujallar Fim kwazo da basira, amin.

Abubakar S. Musa

Fototek Industries Limited, P.M.B.155 Minna, Jihar Neja.

KASH! FURUCIN HADIZA KABARA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA yi matukar gamsuwa game da bayanin edita a kan wasikata ta karshe, kuma ina jiran amsar Hajiya Balaraba Ramat game da bukatar da na gabatar.

2. Abin haushi ne kalamin da Hadiza Kabara ta yi lokacin fadan da suka yi da Saratu Gidado a kan wai Saratu na zargin wani darakta yana kwana da ita Hadiza din. Idan aka yi la'akari da yadda mafi yawancin jama'a suke kallon matan industiri a matsayin marasa mutunci, to wannan zai iya tabbatar masu da gaskiyar zargin da suke yi ma duk wata mai wannan harka ko da kuwa ba hakan suke ba. Saboda haka ya zama dole su san abubuwan da ke fita a bakunasu idan ma har dole ne sai sun furta din.

Dabi'ar nan ma ta fadace- fadace a kan saurayi ko gulmace-gulmace ba a san bahaushiya, kamila, mai mutunci kuma Musulma mai ikirarin wai tana fadakarwa ba da irinta. Haba, kar ku zama 'yan Nigerian film mana! Edita, mun gode Allah ya saka da alheri, amin.

Maryam Garba Jumare

CABS, Kaduna Poytechnic, Kaduna.

ADIRESHIN BIBA DA NA HAMISU

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DON Allah ina so ku ba ni adireshin Hauwa Ali Dodo da Hamisu Iyan-Tama da gaggawa. Na rubuto wannan wasika ne daga kasar Burkina Faso.

Mohammed Abdullahi Yakasai

Adireshin Hamisu Iyan-Tama shi ne: Iyantama@yahoo.com. Ita kuma Hauwa ba mu da nata, amma in ka aiko mata da wasika za mu ba ta.

ANA KALLON FIM A BULGERIYA

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DALILIN da ya sa na rubuto maku wannan wasika shi ne ina son in shaida maku da cewa ni haifaffen Jihar Sokoto ne. An haife ni a garin karamar hukumar mulki ta Rabah a shekarar 1983. Na kare makaranta a shekarar 2000 . Ina karatu ne a makarantar koyon likitanci da ke garin Barna a Bulgaria. Kuma lokacin da ina Nijeriya ni ma'abucin kallon finafinan Hausa ne kuma ina sha'awarsu kwarai da gaske. To amma a nan Bulgaria babu finafinan, ta hanyar na'urar komfuta kacal ne muke kallo domin tunawa da gida, kada mu manta da al'adunmu na gida.

Kuma ina son in shaida muku da cewa a nan Bulgaria akwai abokanmu Turawa da yawa wadanda suka kalli fim din Hausa kuma sun yaba da shi kwarai da gaske, har ma wasu daga cikinsu sun yi kwafi wasu kasakasan namu. Daga karshe ina son ku aika mini gaisuwata ga wadannan mutane: Ibrahim Mandawari, Ibro, Ibrahimawa Production, Sani Musa Danja, Hamisu Iyan-Tama, Ishaq Sidi Ishaq, Ciroki, Zulkifilu Muhammad, Ahmed S. Nuhu, Yautai, Ali Nuhu, da sauran 'yan wasan Hausa da ke Nijeriya.

Abubakar Isah Rabah, Medical University, Barna, Bulgaria. tel.: 0035998247029.

KU RIKA SANYA MUJALLA DA WURI

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA jin dadin karatun mujallar Fim, amma me ya sa ba ku canza website dinku a intanet sai bayan mujallar ta dade da fitowa? Ko mutum yana son ya karanta sai koda yaushe ya bude web site din ya same shi tsohuwa ce, kuma ga irinmu da ke ba ma zaune a Nijeriya balle mu saya mu karanta sai kawai a intanet muke iya karanta. Don Allah ina son idan kuka canza mujallarku ku aika mani imel.

Amina Suleman

Daga England

Hajiya, mun aika maki da amsa ta imel dinki kamar haka: Assalamu alaikum. Dalilin da ya sa muke makara wajen sanya mujallar a intanet shi ne saboda akwai wasu masu karatu da dama a nan Nijeriya da kuma Saudiyya da Nijar wadanda ba su sayen mujallar idan har za su iya karanta ta da wuri a intanet. Shi ya sa muka ce bari mu rika yin latti har sai sun sayi kwafe din sannan mu sanya ta a website. Kin san a namu tsarin (saboda rashin ci-gaba ko lattin ci-gaba ta fuskar kayan fasaha) ba za mu iya yin yadda wasu kamfanoni suke yi a kasashe kamar Ingila ko Amerika ba. Sanya mujallar da muke yi a intanet saboda kishin harshen Hausa ne, ba domin mu samu riba ta kudi ba. Ina fatan dai a sabon website dinmu kike ganin mujallar, wato www.fim.tvheaven.com.

Kuma yana da kyau ki rika duba www.kanoonline.com da kuma www.hausafulani.com domin ganin wasu al'amuran da suka shafi kasar Hausa, cikinsu har da batun shirin fim. Wassalam.

KUN BACE DAGA INTANET NE?

ZUWA GA MUJALLAR FIM,

YAU wajen watanni bakwai kenan ban sake ganin mujallar Fim a intanet ba. Tun watan Maris na shekara ta 2002, ban sake ganin wata sabuwar fitowa ta mujallar ba. Me ya sa? Ko kun sami wata matsala ne? Ko kuma kuna ganin abin ba zai dore ba ne? A gaskiya ban ji dadin haka ba! Da a kodayaushe in na tashi daga aiki ko kuma na sami wani dan lokaci nakan karanta mujallar da na yi downloading zuwa www.kanoonline.com, amma yanzu sai na ga canji. Hakan ina ganin zai iya kawo wani rashin cigaba ga ita mujallar da kuma shi kanshi shirin fim na Hausa.

Mustapha Mu'azu

Computer Unit, Media Trust Limited (Publishers of Weekly and Daily Trust newspapers), No. 22, Lusaka Street, Wuse, Zone 6, P.O. Box 6873, Abuja.

Malam Mustapha, muna jin dai kila kana cikin wadanda ba su sayen kwafen mujallar Fim a kasuwa su karanta sai dai su karanta ta a intanet kawai. Idan ba haka ba, ga shi a duk fitowa muna nuna inda mujallar take a intanet, har kuwa a jikin bangonta! To, za ka same ta a intanet a wannan adireshin: www.fim.tvheaven.com. A sha karatu lafiya!

Komawa babban shafinmu           Komawa saman wannan shafin