Free Web Hosting Provider - Web Hosting - E-commerce - High Speed Internet - Free Web Page
Search the Web

Jagorar mujallun Hausa
FITOWA TA 29   Mayu 2002


BABBAN SHAFI
Mu Leka Mu Gani
Zuwa Ga Masu Karatu
Wasiku
Balaraba Muhammad (1983-2002) na 1
Balaraba Muhammad (1983-2002) na 2
Rayuwarmu
Mu Leka Hollywood
Malam Zurke
Mutanen Boye
Bukukuwa
Sauran Labarai
Ra'ayi Ba Gaba ne
Dangane Da Mu
Muhawara a Zauren YAHOO!GROUPS

Wannan wani zaure ne da aka kirkira a dandalin sadarwa na zamani, wato intanet.
An gina zauren ne a kan tsarin 'Groups' na babbar masana'antar sadarwa ta intanet da ke Amerika din nan mai suna Yahoo!
A wannan zauren namu mutane suna tattaunawa ne musamman a kan finafinan bidiyo na Hausa wadanda ake yayin su yanzu.

JE KA TA NAN


Inda za ka samu tsaffin mujallun Fim
 
Je ka Akwai:
Tallar sabon fim din da ya fito!

NORTHERN STAR FILMS

KE GABATAR DA

GAGARABADAU Fostar fim din kenan

Shiryawa: MUJALLAR Fim

Darakta HAFIZU BELLO

Wasa: Sadiya Abdu Rano, Musbahu M. Ahmad, Sani Moda, Aliyu A. Gora, Hindatu Bashir, Isa Ja, A'isha Ibrahim, Mika'il Hassan 'Gidigo,' Baban Mulika, Shu'aibu 'Kumurci', Ashiru Bazanga, Saratu Gidado, Shehu Kano, Galin Money, d.s.

Labari/Tsarawa: Iro mamman;

Daukar Hoton Bidiyo: Yahaya Skito

BABU IRINSA!

Wasu matafiya ne Allah ya hada su tafiya a tsohuwar motar Direba Moda. Kowanensu yana da ra'ayin yadda ya kamata motar ta rika tafiya: wasu na kukan ana bata lokaci, wasu na cewa a rage gudu...

Can a kan hanya, yaran Gagarabadau (su Kumurci) sun tare hanya suna fashi...

Labari ne na soyayya, ban dariya, tada jijiyar wuya, da ban tsoro...

Idan har ka kalli fim din ba ka yi dariya ko ka ji taraddadin sharrin basawan Gagarabadau ba, to za mu biya ka kudinka! Ka tuntube mu ta e-mail dinmu don ka samu naka

 


Balaraba da kanwarta wacce suke uwa daya uba daya, kuma ita ce ta fito a matsayin Balaraba tana karama cikin fim din NABILA.
Hirarraki da magadan Balaraba

Sunan SHU'AIBU LAWAN ba ya bukatar gabatarwa ga masu karatu. Baya ga cewa fitaccen dan wasa ne, shi ne wanda labarinsu ya game ko'ina a kasar nan a watan da ya gabata dangane da rasuwar amaryarsa, fitacciyar 'yar wasa Balaraba Mohammed. Kwana daya da daura auren, amaryar da wasu danginta mutum uku suka riga mu gidan gaskiya ta hanyar mummunan hadarin mota da ya rutsa da su a kan hanyarsu ta zuwa Kano daga Kaduna.

A wancan lokacin Shu'aibu ya ga fari ya kuma ga baki: farin cikin aurensa da kuma bakin cikin rabuwa da masoyiyarsa. Mujallar Fim ta kawo cikakkaen bayani a kan bikin da kuma mummunan labarin a watan jiya. Sai dai an rage abu daya: ba ku ji ta bakin Shu'aibu ba ko kuma halin da ya shiga a sakamakon abin bakin cikin da ya faru, kuma ba ku ji ta bakin surukansa ba. Dalilin rashin jin takamaiman abin da Shu'aibu yake ciki ya sa dimbin jama'a suka yi ta yada ji-ta-ji-ta a kansa. Daga masu cewa shi ma ya yi hadari ya mutu, sai masu cewa wai ya kuma kansa da bango ya gigita an kwantar da shi a asibiti, kuma wasu suka ce wai ya zautu; wasu har gida sukan same shi don su yi masa ta'aziyyar ganinsa da ido.

"Ashafa, ka san abin da ke kawo wasu 'yan mata nan gidan?"

Wannan tambayar ce Shu'aibu ya yi mani lokacin da na je muna tattaunawa.

Ya ci gaba da cewa, "To wallahi labari ake kai masu cewa wai na zautu ko na haukace; shi ne ya sa suke zuwa don su kalli mahaukaci."

Shu'aibu dai bai haukace ba; ya samu kansa a cikin wani hali wanda zai fi kyau ku karanta ku ji dalla-dalla daga bakinsa. A cikin hirar da ke cikin wannan mujallar babu abin da Kumurci ya rufe sai fa wanda bai sani ba kan tsakaninsa da Balaraba. Duk za ku ji har yadda tun kafin a daura auren ta yi masa bayani kan wasu mutane da suka ce "ba za ta wuce kwana uku ba idan an daura mata aure da Kumurci."

Ban da Shu'aibu, akwai iyayen marigayiya Balaraba. Su ma ba ku ji ta-bakinsu ba a kan mutuwar 'ya'yansu a fitowarmu ta watan jiya. Mun yi duk bakin kokarinmu don samun jin ta-bakinsu, amma abin ya faskara a lokacin saboda suna cikin mawuyacin hali, har an kwantar da su a asibiti. Akwai lokacin da mahaifin marigayiya Balaraba da yayarta marigayiya Jummai, Malam Muhammadu Kaura, ya dan yi wa wakilinmu Aliyu Abdullahi Gora II bayanai a asibiti jim kadan bayan rasuwar. To amma sai ya ce bai so Gora ya dauki bayanan a faifai har sai can gaba. Ya tabbatar masa da cewa za su tattauna.

To, sun tattauna din kuwa. Bugu da kari, Gora ya samu damar tattaunawa da mahaifiyar amaryar da yayarta, wato Malama Binta. Sa'annan marubucinmu na musamman, Shafi'u Magaji Usman (editan mujallar Bidiyo), ya tattauna da limamin masallacin Alhaji Sani Zangon Daura da ke kusa da gidan su Balaraba, wanda shi ne ya koyar da ita karatun allo, kuma shi ne ya daura mata aure, sa'annan shi ne ya sallaci gawarta. Duk a cikin wannan fitowar za ku ji bayanan wadannan bayin Allah wadanda babu abin da za mu yi masu illa addu'a da ci gaba da tausaya masu kan abin da ya faru gare su wanda mu ma duk ya shafe mu a matsayinmu na abokai kuma masoyan Balaraba.

Hasali ma dai yadda abin ya shafe mu din ne ya sa muka yanke shawarar ci gaba da kaddamar da Gidauniya ta musamman don tara wani abu na taimako da za mu mika ga hannun magadan Balaraba. Akwai bayanin gidauniyar a cikin mujallar. Muna fatan ku da sauran jama'a za ku taimaka bakin iyawarku. Malamai sun ce mana yin hakan ba laifi ba ne, kuma duk wanda ya taimaka, sakayyarsa tana wurin Allah.

Idan kun duba sauran shafukanmu kuma za ku samu sauran labarai da bayanai masu gamsarwa kamar yadda kukan samu a kowane wata. Misali, me ya yi zafi har mijin marigayiya Jummai Mohammed ya kai wasu 'yan fim na Kano kara a Abuja bayan rasuwar su Balarabar? Kuma me ya yi zafi har aka mari Rukayya Dawayya a Zariya?

A sha karatu lafiya. Kuma Allah ya kai mu watan gobe ku sha wasu labaran.

Komawa babban shafinmu           Komawa saman wannan shafin